Home Labarai An kama ‘yan daba da masu ƙwacen waya 98 a Kaduna

An kama ‘yan daba da masu ƙwacen waya 98 a Kaduna

Gwamnatin jihar Kaduna ta tabbatar da kama ‘yan daba da masu ƙwacen wayoyi da aka fi sani da ‘yan ‘Sara-Suka’ 98 a jihar.

Gwamnan jihar Mallam Nasir El-Rufai ne ya buƙaci ɗaukar tsattsauran mataki kan ɓata-garin, sakamakon ƙaruwar ayyukan ‘yan daba da masu ƙwacen wayoyi a ƙwaryar birnin Kaduna.

Cikin wata sanarwa da kwamishinan tsaro da al’amuran cikin gida na jihar Samuel Aruwan ya fitar ya ce an gurfanar da 19 daga cikinsu a gabon kotu, yayin da ake ci gaba da bincike kan mutane 61, kafin a gurfanar da su.

Ɓata-garin kan farmaki mutane tare da ƙwace musu wayoyi da sauran kayayyaki, lamarin da ya yi sanadiyyar rasa rayuka tare da jikkata mutane masu yawa.

Rahoton kamen wanda ‘yan sanda suka fitar, ya ce an kama ‘yan dabar a ranakun 26 da 28 ga watan Afrilu.

Rahoton ya ce 18 daga cikin ɓata-garin an kai su sashen binciken manyan laifuka na rundunar ‘yan sandan jihar domin faɗaɗa bincike, gabanin gurfanar da su a gaban kotu.

Gwamnan jihar ya umarci rundunar ‘yan sandan da su tabbatar da yin abin da ya dace domin gurfanar da su a gaban kotu, tare da faɗaɗa bincike don kamo duk masu aikata irin wannan ta’asa a faɗin jihar.

El-Rufai ya kuma jajanta wa iyalan waɗanda suka rasa rayukansu, tare da fatan samun sauƙi ga waɗanda suka jikkata, sanadiyyar ayyukan ‘yan bindigar.

Daga ƙarshe gwamnan ya yi kira ga al’umma musamman mazauna unguwannin da ake wannan ta’asa da su kai sunayen ‘yan dabar da ke addabar yankunansu ga jami’an tsaro domin a bibiye su.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp