Home Labarai Gwamnatin jihar Bauchi za ta ƙirƙiro rundunar tsaro ta musamman

Gwamnatin jihar Bauchi za ta ƙirƙiro rundunar tsaro ta musamman

Gwamnatin Bauchi ta ce za ta dauki matasa akalla dubu 20,000 aiki domin yakar matsalar tsaro da tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali, karkashin wata rundunar tsaro da za ta kirkiro ta musamman a jihar.

An ruwaito cewa rundunar tsaron za ta kasance ne kamar wadda jihohin kudu maso yammacin kasar suka kirkiro wadda ake kira Amotekum.

Gwamnan jihar Sanata Bala Abdulkadir Mohammed, ne ya bayyana matakin jim kadan da sake rantsar da shi a wa’adi na biyu a matsayin gwamnan a jiya Litinin.

Mai sharia Rabi Talatu ce ta rantsar da shi tare da mataimakinsa Mohammed Auwal Jatau a lokacin.

Gwamnan ya ce rundunar wadda za ta taimaka gaya ga tsarin tsaron da tuni ake da shi a kananan hukumomin jihar za ta kunshi matasa 20,000 da za a fara dauka a kashin farko.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp