Sojojin Nijeriya sun hallaka ‘yan bindiga 36 tare da kwato mutane 140 – DHQ

Shalkwatar rundunar sojin Nijeriya tace cikin makwanni 2 dakarunta sun sami nasarar kame ‘yan ta’adda 137 tare da hallaka’ 36 a fadin kasar.

Haka Kuma cikin makwanni biyun ta sami nasarar ceto mutane 140 daga hannun ‘yan bindigar.

Daraktan sashen yada labaran shalkwatar Manjo Janar Edward Buba, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwar mako – mako da ya fita a birnin tarayya Abuja.

Yace a yayin atisayen dakarun sun kama’ yan bindiga 3, masu garkuwa da mutane 2, sai wadanda ake hadin baki da su mutum 6 sai kuma barin danyen mai su 15 inda suka samu kudi har naira 3,177,650.00.

Janar Buba yace maza da mata a a cikin dakarun sojin Nijeriya sun shirya yaki da dukkan aikin bata gari.

“a shirye muke mu yake su, ya zama waji mu kakkabe su daga cikin mu.”

Yace a cikin makwanni dakarun sun sami nasarar kwato makamai 37 da alburusai 370, bindiga kirar ak47 guda 16, bindiga kirar pump action guda 6, kirar dane guda sai kuma karamar bindiga kirar gida 2 da dai sauran muggan makamai.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 22 minutes 5 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 3 minutes 30 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com