Home Labarai Har yanzu shigowa da shinkafa Nijeriya daga waje laifi ne – Tinubu

Har yanzu shigowa da shinkafa Nijeriya daga waje laifi ne – Tinubu

Fadar shugaban Nijeriya ta ce umarnin bude iyakokin kasar da jamhuriyar Nijar da Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya bayar, ba wai yana nufin bada damar shigo da kayan masarufi da sauran kayayyakin da tsohuwar gwamnatin Buhari ta hana shigo da su kasar ba ne.

”Wannan umarnin yana magana ne kawai akan abubunwan da suka faru ko matakan da ECOWAS ta dauka na sanyawa ƙasar Nijar takunkumi sakamakon Juyin mulki da sojojin kasar suka yi, don haka umarnin shugaban kasar yana magana ne kawai a koma Inda ake a bara “.

Babban Mai taimakawa shugaban kasa kan harkokin yada labarai Abdulaziz Abdulaziz ne ya bayyana hakan, yayin da yake Karin bayani ga manema labarai ta wayar tarho dangane da umarnin da shugaban kasa Bola Tinubu ya bayar na bude iyakokin Nigeria da jamhoriyar Nijar.

Yace umarnin ba wai yana nufin a cigaba da shigo da kayan masarufi da sauransu ba ne, “dokokin mu na cikin gida na hukumar kwastam suna nan kuma jami’an hukumar zasu cigaba sa sanya idanu akan duk kayan da za’a Shigo da su Nijeriya.

”Kamar yadda aka sani a dokokin hukumar Kwastam akwai kayan da aka aminta da su akwai kuma wadanda ba’a aminta a shigo da su ba, don haka dokar da aka sa a baya tana nan tana aiki musamman akan shinkafa da wasu sauran abubuwan amfani na yau da kullum har yanzu dokar tana nan tana aiki aka su”.

Idan za’a iya tunawa tsohon shugaban kasar Nijeriya Muhammad Buhari shi ne ya rufe iyakokin kasar inda aka hana shigo da Shinkafa, kayan masarufi da sauransu da nufin inganta wadanda ake samar wa a cikin gida Nigeria.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp