Home Labarai Rundunar Sojin saman Nijeriya ta kone jiragen ruwan dakon Danyen Mai a...

Rundunar Sojin saman Nijeriya ta kone jiragen ruwan dakon Danyen Mai a Neja Delta

Dakarun sojin saman Najeriya da ke aiki ƙarƙashin rundunar ‘Operation Delta Safe’ sun sami nasarar tarwatsa wuraren tace mai ba bisa ƙa’ida ba da jiragen ruwan dakon kaya maƙare da ɗanyen mai da aka sace a yankin Neja Delta.

wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da daraktan yaɗa labarai na rundunar sojin saman Najeriya, Edward Gabkwet, ya fitar wadda ta ce a yayin wani samame da dakarun suka kai kan cibiyoyin da jiragen ruwan dakon kayan tsakanin 25 da 26 ga watan Maris a wasu yankunan jihar Rivers.

An gano wani jirgin dakon kaya a yankin Bille cike da albarkatun mai da aka tace ba bisa ƙa’ida ba. Kazalika, sojojin a yankin Dariama da Tumakiri, wuraren da suka yi suna kan tace mai ba bisa ƙa’ida ba, sojojin sun gano tukwanen girki abin da ke nuna akwai mutane a wajen. Sun kuma yi musayar wuta tsakaninsu inda kuma suka lalata wuraren da ake tace man ba bisa doka ba.

A cewar sanarwar, sojoji sun ƙona wasu wuraren da aka gano ana tace ɗanyen mai ba bisa ƙa’ida ba inda kuma aka cinna masu wuta.

A baya, sojoji sun lalata wuraren da aka gano a Bille da Dariama. Rundunar sojin saman da wasu hukumomin tsaro, a cewar sanarwar za su ci gaba da ƙara ƙaimi wajen gano ayyukan masu satar ɗanyen ma da ke gudanar da ayyukansu a yankin.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp