Home Labarai Ta kashe mijinta mai cutar shanyewar ɓarin jiki, ta jefar da gawarsa...

Ta kashe mijinta mai cutar shanyewar ɓarin jiki, ta jefar da gawarsa a kango

Ana zargin wata mata mai suna Rahimat Salaum da kashe mijinta mai fama da larurar shanyewar ɓarin jiki sannan ta jefar da gawarsa a cikin wani kango.

Lamarin ya faru ne a yankin Pegi da ke Babban Birnin Tarayya Abuja.

Kakakin rundunar ’yan sanda ta shiyyar Abuja, SP Josephine Adeh, ita ce ta tabbatar da hakan a cikin wata sanarwa da yammacin Talata.

Ta ce tuni jami’an rundunar da ke yankin na Pegi ne suka cafke Rahimat a ranar Litinin.

A cewar Josephine, an kama matar ne lokacin da take ƙoƙarin tserewa da kayayyakin mijin nata, kafin ’yan sanda su yi mata ƙofar-rago su kama ta.

“Bayan an yi mata tambayoyi, wacce ake zargin ta amsa cewa ita ce ta kashe mijin nata bayan wata sa’insa da ta shiga tsakaninsu. Daga nan ne ta yi wa jami’anmu jagora zuwa kangon da ta jefar da gawar tasa, inda aka tarar da shi ya yi mummunar ƙonewa,” in ji Kakakin ’yan sandan.

Sai dai ta ce ’yan sanda na ci gaba da gudanar da bincike a kan lamarin, kuma da zarar sun kammala za su miƙa ta gaban kotu domin ta girbi abin da ta shuka.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp