Home Labarai ‘Yan Ta’adda sun yi garkuwa da daliban lafiya a jihar Benuwai

‘Yan Ta’adda sun yi garkuwa da daliban lafiya a jihar Benuwai

Rahotannin daga jihar Benuwai a Arewa maso tsakiyar Nijeriya na bayyana cewa wasu ‘yan bindiga sun kai hari, inda suka yi garkuwa da ɗalibai da wani ɗalibin likitanci mai sanin makamar aiki a jihar da ke fama da matsalar ƴan bindiga.

An kai wa ɗaliban harin ne a lokacin da suke hanyarsu ta zuwa Kudu maso Gabashin Jihar Enugu a ranar 15 ga watan domin halartar taron Ƙungiyar Ɗaliban Likitanci na shekara-shekara.

“Daliban, waɗanda aka ce ƴan Jami’ar Maiduguri da Jami’ar Jos ne, suna tafiya ne a tare, inda ƴan bindigar suka afka musu da misalin ƙarfe 3:30 na yamma a yankin Otukpo na jihar.”

Kakakin Rundunar ‘Yan sanda, Catherine Anene, ta ce ana ci gaba da gudanar da bincike a kan lamarin.

Harkar garkuwa da mutane ba sabon abu ba ne a Najeriya, inda lamarin ya fara zama ruwan dare a ƙasar ta Afirka ta Yamma.

A watan Mayu, ƴan bindiga sun kashe mutum 11, sannan suka sace wasu da ba a tantance adadinsu ba a Ƙaramar Hukumar Agatu ta Jihar Benue.

Haka kuma a Janairu, aƙalla fasinjoji guda 45 ne aka sace a lokacin da ƴan bindiga suka tare wasu motoci a kan hanyar Otukpo-Enugu.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp