Home Labarai ‘Yan Ta’adda sun yi garkuwa da daliban lafiya a jihar Benuwai

‘Yan Ta’adda sun yi garkuwa da daliban lafiya a jihar Benuwai

Rahotannin daga jihar Benuwai a Arewa maso tsakiyar Nijeriya na bayyana cewa wasu ‘yan bindiga sun kai hari, inda suka yi garkuwa da ɗalibai da wani ɗalibin likitanci mai sanin makamar aiki a jihar da ke fama da matsalar ƴan bindiga.

An kai wa ɗaliban harin ne a lokacin da suke hanyarsu ta zuwa Kudu maso Gabashin Jihar Enugu a ranar 15 ga watan domin halartar taron Ƙungiyar Ɗaliban Likitanci na shekara-shekara.

“Daliban, waɗanda aka ce ƴan Jami’ar Maiduguri da Jami’ar Jos ne, suna tafiya ne a tare, inda ƴan bindigar suka afka musu da misalin ƙarfe 3:30 na yamma a yankin Otukpo na jihar.”

Kakakin Rundunar ‘Yan sanda, Catherine Anene, ta ce ana ci gaba da gudanar da bincike a kan lamarin.

Harkar garkuwa da mutane ba sabon abu ba ne a Najeriya, inda lamarin ya fara zama ruwan dare a ƙasar ta Afirka ta Yamma.

A watan Mayu, ƴan bindiga sun kashe mutum 11, sannan suka sace wasu da ba a tantance adadinsu ba a Ƙaramar Hukumar Agatu ta Jihar Benue.

Haka kuma a Janairu, aƙalla fasinjoji guda 45 ne aka sace a lokacin da ƴan bindiga suka tare wasu motoci a kan hanyar Otukpo-Enugu.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
COAS Ya Bukaci Bojojin Nijeriya da su Mayar da Hankali Wajen Kare Rayukan Fararen HulaTURA TA KAI BANGO: Bayan Mutuwar Bashar Sani, Dole ne Arewa Ta Fuskanci MatsalolintaDangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige Fubara
X whatsapp