‘Yan Ta’adda sun yi garkuwa da daliban lafiya a jihar Benuwai

Rahotannin daga jihar Benuwai a Arewa maso tsakiyar Nijeriya na bayyana cewa wasu ‘yan bindiga sun kai hari, inda suka yi garkuwa da ɗalibai da wani ɗalibin likitanci mai sanin makamar aiki a jihar da ke fama da matsalar ƴan bindiga.

An kai wa ɗaliban harin ne a lokacin da suke hanyarsu ta zuwa Kudu maso Gabashin Jihar Enugu a ranar 15 ga watan domin halartar taron Ƙungiyar Ɗaliban Likitanci na shekara-shekara.

“Daliban, waɗanda aka ce ƴan Jami’ar Maiduguri da Jami’ar Jos ne, suna tafiya ne a tare, inda ƴan bindigar suka afka musu da misalin ƙarfe 3:30 na yamma a yankin Otukpo na jihar.”

Kakakin Rundunar ‘Yan sanda, Catherine Anene, ta ce ana ci gaba da gudanar da bincike a kan lamarin.

Harkar garkuwa da mutane ba sabon abu ba ne a Najeriya, inda lamarin ya fara zama ruwan dare a ƙasar ta Afirka ta Yamma.

A watan Mayu, ƴan bindiga sun kashe mutum 11, sannan suka sace wasu da ba a tantance adadinsu ba a Ƙaramar Hukumar Agatu ta Jihar Benue.

Haka kuma a Janairu, aƙalla fasinjoji guda 45 ne aka sace a lokacin da ƴan bindiga suka tare wasu motoci a kan hanyar Otukpo-Enugu.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 18 minutes 57 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 22 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com