Gwamnan Kano ya bayar da umarnin bincikar badakar sayen magunguna a jihar

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya bayyana cewa bashi da masaniya kan kwangilar samar da magunguna a kananan hukumomi 44 na jihar.

wannan na cikin wata Sanarwar da kwamishinan yada Labarai na jihar Baba Halilu Dan Tiye ya fitar wadda aka rabawa manema labarai, ta ce Gwamnan Abba ya umurci Shugaban Hukumar karbar Korafe-korafe da Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Kano da ta gaggauta bincikar wannan zargi tare da bayar da rahoton sakamakon da ya dace domin daukar matakin da ya dace.

Sanarwar ta ci gaba da cewa manufar binciken shine bankado gaskiyar Lamarin domin tabbar da gaskiya da rikon amana wajen gudanar da shugabanci na gari ga alummar Kano baki daya.

Daga bisani Gwamna Yusuf ya kuma bukaci daukacin al’ummar Kano da su yi hakuri har a kammala bincike.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 6 minutes 31 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 10 hours 47 minutes 56 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com