Boko haram ta hallaka Masallata 34 a jihar Yobe

Wani harin mayakan boko haram kan masallata yayi sanadiyyar mutuwar mutane 34, a garuruwan Mafa, Tarmuwa dake jihar Yobe a arewa maso gabashin Nijeriya.

Mayakan na boko haram sun isa wani masallaci yayin da al’umma ke tsaka gudanar da sallah Magriba, in suka ka su da harbin kan mai uwa da wabi a ranar lahadin data gabata.

Mai sharhi kan al’amurarran da suka shafi tsaro a yankin tafkin Chadi Zagazola Makama, ya ruwaito cewa harin na matsayin martanin mayakan boko haram kan Al’ummar yankin bisa kin biyan harajin da suka yi ga kungiyar dake tayar da kayar bayan a yankin.

Yace aboye al’ummar garin na biyan mayakan na boko haram haraji ba tare da sanin jami’an tsaro ba, wannan ne yasa mayakn na boko haram kai musu mummunan harin da yayi sandiyyar mutuwar mutane.

Haka kuma rahoton yace a wani yunkuri na tsananta lamarin mayakan sun binne wasu abubuwan fashewa guda hudu akan hanya domin harar dakarun da zasu kawo dauki bayan sun kamala gudanar da ta’addancin kan Al’ummar.

Wannan harin na boko haram ya sake fito da matsin da suke kara fuskanta a wajen jami’an tsaro, tare da fito da bukatar dake akwai na sake bawa dakarun sojojin bayanan sirrin don dakile ayyukan ‘yan ta’addan.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 4 hours 34 minutes 48 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 6 hours 16 minutes 13 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com