Home General Daurarru na mutuwa saboda yunwa a gidajen yarin Nijeriya

Daurarru na mutuwa saboda yunwa a gidajen yarin Nijeriya

Hukumar dake lura da gidan ajiya da gyaran hali ta Calabar dake jihar cross river ta ce ta na bincike kan  matsalar ciyar da daurarru dake ajje a gidan domin tabbatar da walwalar su.

Kakakin hukumar na jihar Abubakar Umar ne ya bayyana hakan yayin da yake ganawa da kamfanin dillanci labarai na Nijeriya NAN a birnin Abuja ranar talata.

Inda yace ministan cikin gida na Olubunmi Tunji-Ojo, ya bayar da umarnin a gudanar da bincike kan zargin badakala a harkokin ciyar da daurarru a gidan ajiya da gyaran hali na Afokang dake tsakiyar Calabar a jihar Cross River.

Umarnin na zuwa ne bayan wani faifan bidiyo daya fito kan yadda ake lura da daurarrun, wanda ciki harda yadda ake basu wani wake da bai dahu ba a lokacin Karin kumallo.

Ko dai ta cikin wani sako da Dan jarida Ja’afar Ja’afar Ya wallafa a shafinsa na facebook ya bayyana yadda wani ma’aikacin gidan gyaran hali da tarbiyya ya aike masa da wani sako kan halin da daurarru ke ciki a gidan ajiya da gyaran hali.

Sakon yace “Sir mutane na mutuwa a Prison saboda yunwa” “Wallahi a inda nake aiki kullum sai an fita da gawa” “kuma Yunwa ce”.

“sun hana kowa shiga da Phone (waya) don kada a dauki hoton abinci”

“hoton dake yawo na calaba Prison to kusan duk sauran prison din haka suke babu abinci”

“Staff wani lokacin ke taimakon Inmate da abinci da ga cikin salary su” “wallahi ko ni kusan duk sati sai na sayi kuli-kuli da garin rogo na rabawa inmate”.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp