Home General Jam’iyyar APC ta jefa kanta cikin halaka – Kwankwaso

Jam’iyyar APC ta jefa kanta cikin halaka – Kwankwaso

Jagoran jam’iyyar NNPP a Najeriya, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya ce jam’iyyar PDP mai hamayya a ƙasar ta mutu a fagen siyasar ƙasar.

Yayin da yake jawabi a ofishin jam’iyyar NNPP na jihar Katsina ranar Asabar, jagoran Kwankwasiyyar ya zargi jam’iyyar APC ta jefa kanta cikin abin da ya kira ”halaka”.

”Jam’iyyar PDP dama kowa ya sani a yanzu dai matacciya ce, dama mu ne a cikinta, kuma tun da ta saki layi, muka sake”, in Sanata Kwankwaso.

Ya kuma zargi jagororin gwamnatin APC da nuna halin ko- in-kula game da halin da ƙasar ke ciki, musamman ta fuskar matsalar rashin tsaro.

”Kuna gani yanzu idan kana son fita daga cikin Katsina, duk inda za ka bi, to tunani kake ta inda za ka bi”. in ji shi.

Sanata Kwankwaso ya kuma yi kira ga talakawan Najeriya su kauce wa karɓar taliya ko wasu kuɗi da ya ce ba su taka kara suka karya ba a ranar zaɓe domin sarayar da haƙƙoƙinsu.

”Ku tabbatar cewa ba a sake kawo taliya mutane sun karɓa, sun je sun dafa, sun ci, sun kuma faɗa wahala na shekara huɗu su da ‘ya’ya da jikoki, kun dai ga duka wannan wahalar a kan talaka take ƙarewa,” in ji jagoran Kwankwasiyyar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp