Hukumar bayar da agajin gaggawa ta ƙasa (NEMA) ta ce ta fara kai agaji domin kwashe mutanen da ambaliyar ruwa ta ɗaiɗaita a Maiduguri, babban birnin jihar Borno; ambaliyar ta biyo bayan fashwar madatsar ruwa.
Wannan dai na cikin wata sanawar da babbar darektar hukumar Zubaida Umar ta fitar a shafinta na X, ta ce sun kuma fara shirye-shiryen tallafa wa mutanen da lamarin ya shafa da abinci, matsuguni da kuma magaunguna.
Yankunan da ambaliyar ta shafa sun haɗa da Shehuri, rukunin gidaje da ke G.R.A, Gambomi, Budum, Bulabulin, Adamkolo, Millionaires Quarters, kasuwar Monday Market da kuma Gwange.
NEMA ta ce gwamnatin jihar Borno ta buɗe sansanin Bakassi domin tsugunar da mutanen da ambaliyar ta shafa.
Ta ce suna aiki da hukumar ba da agaji reshen jihar ta Borno domin tallafa wa mutanen da ke cikin sansanin.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1462 days 18 hours 29 minutes 32 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1444 days 20 hours 10 minutes 57 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com