Home AFIRKA ‘Yansanda sun kama masu zanga-zanga 42 a Ghana

‘Yansanda sun kama masu zanga-zanga 42 a Ghana

‘Yan sanda a Ghana sun ce sun damke mutane 42 cikin masu zanga-zanga a Accra, babban birnin ƙasar..

Hakan ya biyo rikicin da ya faru bayan cin karo da ƴansanda da masu zanga-zangar suka yi.

Suna zanga-zangar ce domin nuna damuwa game da matsin tattalin arziki.

Tun a ranar Juma’a suka fara zanga-zangar kuma ana sa ran za su ci gaba a yau Litinin.

Masu zanga-zangar waɗanda galibinsu matasa ne sun yi maci a cikin birnin Accra suna wakoki tare da ɗaga kwalaye, inda suke suna damuwa kan irin ɓarnar da hako ma’adinai ta ɓarauniyar hanya ke yi wa muhalli.

Matasan kuma na ganin cewa gwamnati na almubazzaranci da kuɗaɗen da ake samu a harkar ma’aidinai.

Sanarwar da ‘yan sanda suka fitar ta ce mutane 42 ne aka tsare kawo yanzu.

Kakakin ‘yan sandan, Grace Ansah Akrofi ta ce za a gurfanar da matasan a gaban kuliya bisa zargin kawo tsaiko a kan hanya da kuma lalata dukiyar gwamnati da kuma tayar da hankali.

A cewar ‘yan sandan, masu zanga-zangar sun saɓa doka saboda cire makullin motar ‘yan sanda tare da jefar da makullin sannan kuma sun ture shingen da jami’an tsaro suka saka.

A halin yanzu, ‘yan sandan na neman ɗaya daga cikin shugabannin masu zanga-zangar Oliver Barker Vormawor saboda laifin guje wa kame.

Sai dai jagoran masu zanga-zangar ya musanta zargin inda ya ce maganar ‘yan sandan ba ta da tushe.

A martaninta, ƙungiyar Democracy Hub wadda ke kan gaba wajen shirya wannan zanga-zangar, ta yi Alla-wadai kan yadda ‘yan sanda suka yi amfani da karfi da kuma abin da ta kira dirar mikiya kan masu zanga-zangar lumana.

Zanga-zangar na zuwa ne a daidai lokacin da ake shirin gudanar da zaɓen shugaban ƙasa a watan Disamba kuma batun tattalin arziki shi ne ya kankane yaƙin neman zaɓen ƙasar.

Manyan ‘yan takara biyu a zaɓen su ne mataimakin shugaban ƙasa, Mahamudu Bawumia na jam’iyyar NPP mai Mulki da kuma tsohon shugaban ƙasa, John Mahama na NDC.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp