Home General Tinubu ya taya Monday Okpebholo murnar lashe zaɓen gwamnan Edo

Tinubu ya taya Monday Okpebholo murnar lashe zaɓen gwamnan Edo

Shugaba Bola Tinubu ya taya zaɓaɓɓen gwamnan jihar Edo, Monday Okpebholo murnar lashe zaɓe.

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta INEC ce ta sanar da Okpebholo matsayin wanda ya lashe zaɓen da aka gudanar ranar Asabar 21 ga watan Satumba, inda ya doke sauran ƴan takara.

Wata sanarwa da mai bai wa shugaban shawara kan harkar yaɗa labarai Bayo Onanuga ya fitar a shafinsa na X, Tinubu ya yaba wa jagorancin jam’iyyar APC na ƙasa da kuma gwamnonin jam’iyyar bisa jajircewarsu wajen ganin an samu nasara.

Ya buƙaci sabon gwamnan jihar ta Edo da ya ɗauki nasarar a matsayin hakki da aka ɗora masa wajen kai jihar gaba.

“Nasarar ta nuna irin goyon baya da mutane ke yi wa jam’iyyar mu ta APC, ƙoƙari da take yi da kuma tsare-tsare da take ɓullo da su wajen inganta rayuwar ƴan Najeriya,” in ji Tinubu.

Ya ce Okpebholo ya nuna dattako wajen gayyato ƴan adawa domin a yi tafiya tare da kuma haɗa kan al’ummar jihar don samun ci gaba.

Shugaban Najeriyar ya kuma yaba yadda aka gudanar da zaɓen cikin kwanciyar hankali da lumana.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp