Home General Tinubu ya taya Monday Okpebholo murnar lashe zaɓen gwamnan Edo

Tinubu ya taya Monday Okpebholo murnar lashe zaɓen gwamnan Edo

Shugaba Bola Tinubu ya taya zaɓaɓɓen gwamnan jihar Edo, Monday Okpebholo murnar lashe zaɓe.

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta INEC ce ta sanar da Okpebholo matsayin wanda ya lashe zaɓen da aka gudanar ranar Asabar 21 ga watan Satumba, inda ya doke sauran ƴan takara.

Wata sanarwa da mai bai wa shugaban shawara kan harkar yaɗa labarai Bayo Onanuga ya fitar a shafinsa na X, Tinubu ya yaba wa jagorancin jam’iyyar APC na ƙasa da kuma gwamnonin jam’iyyar bisa jajircewarsu wajen ganin an samu nasara.

Ya buƙaci sabon gwamnan jihar ta Edo da ya ɗauki nasarar a matsayin hakki da aka ɗora masa wajen kai jihar gaba.

“Nasarar ta nuna irin goyon baya da mutane ke yi wa jam’iyyar mu ta APC, ƙoƙari da take yi da kuma tsare-tsare da take ɓullo da su wajen inganta rayuwar ƴan Najeriya,” in ji Tinubu.

Ya ce Okpebholo ya nuna dattako wajen gayyato ƴan adawa domin a yi tafiya tare da kuma haɗa kan al’ummar jihar don samun ci gaba.

Shugaban Najeriyar ya kuma yaba yadda aka gudanar da zaɓen cikin kwanciyar hankali da lumana.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp