Home General Ambaliyar Maiduguri: Zulum ya kafa kwamitin rabon tallafi

Ambaliyar Maiduguri: Zulum ya kafa kwamitin rabon tallafi

Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya kafa kwamitin rabon kayan tallafi ga mutanen da iftila’in ambliya ya shafa a Maiduguri, babban birnin jihar.

Wata sanarwa da sakataren gwamnatin jihar Bukar Tijjani ya fitar, gwamna Zulum ya ce kwamitin mai mamboi 35 zai kunshi wakilai daga hukumomi da dama da suka haɗa da hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC da takwararta ta ICPC da kuma hukumar tsaro ta farin kaya wato DSS.

Sauran mambobin kwamitin sun haɗa masu ba shi shawara da wakilan hukumar raya yankin arewa maso gabas (NEDC), ma’aikatar wasanni da ci gaban matasa da ma’aikatar kudi da ta mata da kuma hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar (SEMA) da sauransu.

Gwamna Zulum ya buƙaci mambobin kwamitin da su jajirce wajen sauke nauyin da aka ba su da kuma yin gaskiya.

“Za mu tabbatar da cewa an yi amfani da kuɗin ta hanyar da ya dace, za mu tsaya mu ga tallafin ya kai ga mutanen da aka yi domin su,” in ji Zulum.

Ya ce gwamnatin jihar za ta tabbatar da ganin an sake gyara wurare kamar asibitoci da hanyoyi da kuma gadoji.

Mutane da dama dai, musamman masu hannu da shuni suka bayar da tallafin kuɗaɗe da kuma kayan abinci zuwa ga waɗanda ambaliyar Maiduguri ta shafa.

Ya ce sun samu karɓar tallafi da ya kai naira biliyan 4.4 zuwa cikin asusun tallafin jihar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp