Home General Yiaga Africa ta ce an yi Magudi a zaben jihar Edo

Yiaga Africa ta ce an yi Magudi a zaben jihar Edo

Kungiyar ci gaban al’umma ta Yiaga Africa ta caccaki sakamakon zaɓen gwamnan jihar Edo da aka gudanar a ranar Asabar, tana mai cewa zaɓen ya gaza cika ƙa’idar gaskiya da amana.

Cikin wata sanarwa da ta fitar a yau Litinin, wadda Shugabar tawagar lura da zaɓen Edo na 2024, Dr. Aisha Abdullahi da Daraktan gudanarwarta, Samson Itodo suka sanya wa hannu, sun bayyana cewa zaɓen jihar Edo na 2024 ya gaza cika ƙa’idar gaskiya saboda rashin bayyana gaskiya kan tsarin tattara sakamakon zaɓen.

Ƙungiyar ta ce yayin da aka bi ƙa’idoji a wajen tantance masu zaɓe, yin zaɓe, ƙirga ƙuri’u, da rubuta sakamako a rumfunan zaɓe, an yi maguɗi a wajen tattara sakamakon zaɓe sakamakon haɗin kai tsakanin wasu jami’an zaɓe na INEC da wasu mutane.

Wannan maguɗi, in ji su, ya lalata amincin zaɓen gaba ɗaya.

Kungiyar ta yi wannan hukunci ne bayan amfani da dabarar Process and Results Verification for Transparency, PRVT, wajen duba zaɓen gwamnan jihar Edo.

Haka kuma, sun ce sun tura masu sa ido mutum 300 da wasu masu sintiri 25 waɗanda suka zagaye rumfunan zaɓe a dukkan kananan hukumomi 18 na jihar.

Hukumar zaɓe ta INEC ta bayyana ɗan takarar jam’iyyar APC, Monday Okpebholo, a matsayin wanda ya lashe zaɓen bayan ya doke manyan abokan hamayyarsa Asue Ighodalo na PDP da Olumide Akpata na LP.

INEC ta bayyana cewa, ɗan takarar APC ya samu ƙuri’u 291,667, yayin da Ighodalo ya samu ƙuri’u 247,274.

Akpata na LP kuwa ya zo na uku da ƙuri’u 22,763.

Kungiyar Yiaga Africa ta ce ta samu rahotannin maguɗi da tashin hankali a yayin tattara sakamako a kananan hukumomin Ikpoba/Okha, Etsako West, Egor da Oredo.

Sun ce wannan maguɗi ya haɗa da tsoratar da jami’an zaɓe na INEC, masu sa ido, da kuma wakilan jam’iyyu.

Ƙungiyar ta kuma bayyana cewa rahotanninta sun nuna ɓarnar sakamakon da aka yi a wasu rumfunan zaɓe.

Rahoton ya ce akwai bambance-bambance tsakanin sakamakon da aka bayyana da kuma adadin ƙuri’un da aka tattara a rumfunan zaɓe.

Ƙungiyar ta ƙara da cewa wannan maguɗi ya jawo dole a ƙi amincewa da sakamakon ƙarshe na zaɓen.

Duk da haka, Yiaga Africa ta yarda da sakamakon ƙididdigar INEC kan yawan fitowar masu zaɓe da ƙuri’un da aka ƙi karɓa.

Kungiyar ta ce sakamakon INEC ya yi daidai da hasashenta na fitowar masu zaɓe tsakanin kashi 20.9 zuwa 24.1, inda hukumar ta bayyana cewa fitowar masu zaɓe ya kasance kashi 22.4.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp