Home General Sakamakon zaben Gwamna a wasu kananan hukumomi na jihar Edo

Sakamakon zaben Gwamna a wasu kananan hukumomi na jihar Edo

Jam’iyyar PDP mai mulkin jihar Edo ta yi kira ga hukumar zaɓen ƙasar da ta bayyana sakamakon zaɓen da ke kan na’urorin adana sakamakon zaɓe na hukumar wato IREV.

Gwamnan jihar Godwin Obaseki da takwarorinsa na jihohin Adamawa da Taraba ne suka bayyana haka a wani taron manema labarai da suka gabatar a ɗakin tattara sakamakon zaɓe na jam’iyyar wato ‘ PDP Situation Room’.

Gwamnonin uku sun zargi hukumar INEC da rubuta sakamakon da ba na gaskiya ba a kan takardar rubuta sakamakon a wasu rumfunan zaɓen jihar.

Tuni dai hukumar zaɓen ta ce ta ƙaddamar da bincike kan zargin rubuta sakamakon bogin a kan takardun rubuta sakamakon zaɓen.

Sannan ta buƙaci a kwantar da hankali da bin doka da oda da mutunta juna yayin da take dab da fara aikin karɓar sakamakon.

to sai dai tuni hukumae ta INEC ta fara barra sakamakon zaben ina a karamar hukumar Esan ta Yamma

APC – 12952

PDP – 11004

sai kuma karamar hukumar Owan ta Yamma

APC – 12277

PDP – 11284

Karamar hukumar Uhunmwode

APC – 8776

PDP – 9339

a karamar hukumar Ovia ta Arewa maso yamma kuwa

APC – 13225

PDP – 15311

sai kuma karamar hukumar Esan ta kudu maso Gabas

APC – 8398

PDP – 14199

haka kuma hukumar ta INEC ta bayyana sakamakon karamar hukumar Egor inda tace

APC – 16760

PDP – 14658

wadannan dai sakamakon manyan Jam’iyyun siyasa a jihar ne wadanda ke kan gaba wajen yawan kuri’a a zaben da ya guda a ranar asabar a jihar ta Edo.

PRnigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp