Home General Sakamakon zaben Gwamna a wasu kananan hukumomi na jihar Edo

Sakamakon zaben Gwamna a wasu kananan hukumomi na jihar Edo

Jam’iyyar PDP mai mulkin jihar Edo ta yi kira ga hukumar zaɓen ƙasar da ta bayyana sakamakon zaɓen da ke kan na’urorin adana sakamakon zaɓe na hukumar wato IREV.

Gwamnan jihar Godwin Obaseki da takwarorinsa na jihohin Adamawa da Taraba ne suka bayyana haka a wani taron manema labarai da suka gabatar a ɗakin tattara sakamakon zaɓe na jam’iyyar wato ‘ PDP Situation Room’.

Gwamnonin uku sun zargi hukumar INEC da rubuta sakamakon da ba na gaskiya ba a kan takardar rubuta sakamakon a wasu rumfunan zaɓen jihar.

Tuni dai hukumar zaɓen ta ce ta ƙaddamar da bincike kan zargin rubuta sakamakon bogin a kan takardun rubuta sakamakon zaɓen.

Sannan ta buƙaci a kwantar da hankali da bin doka da oda da mutunta juna yayin da take dab da fara aikin karɓar sakamakon.

to sai dai tuni hukumae ta INEC ta fara barra sakamakon zaben ina a karamar hukumar Esan ta Yamma

APC – 12952

PDP – 11004

sai kuma karamar hukumar Owan ta Yamma

APC – 12277

PDP – 11284

Karamar hukumar Uhunmwode

APC – 8776

PDP – 9339

a karamar hukumar Ovia ta Arewa maso yamma kuwa

APC – 13225

PDP – 15311

sai kuma karamar hukumar Esan ta kudu maso Gabas

APC – 8398

PDP – 14199

haka kuma hukumar ta INEC ta bayyana sakamakon karamar hukumar Egor inda tace

APC – 16760

PDP – 14658

wadannan dai sakamakon manyan Jam’iyyun siyasa a jihar ne wadanda ke kan gaba wajen yawan kuri’a a zaben da ya guda a ranar asabar a jihar ta Edo.

PRnigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp