Home General Sakamakon zaben Gwamna a wasu kananan hukumomi na jihar Edo

Sakamakon zaben Gwamna a wasu kananan hukumomi na jihar Edo

Jam’iyyar PDP mai mulkin jihar Edo ta yi kira ga hukumar zaɓen ƙasar da ta bayyana sakamakon zaɓen da ke kan na’urorin adana sakamakon zaɓe na hukumar wato IREV.

Gwamnan jihar Godwin Obaseki da takwarorinsa na jihohin Adamawa da Taraba ne suka bayyana haka a wani taron manema labarai da suka gabatar a ɗakin tattara sakamakon zaɓe na jam’iyyar wato ‘ PDP Situation Room’.

Gwamnonin uku sun zargi hukumar INEC da rubuta sakamakon da ba na gaskiya ba a kan takardar rubuta sakamakon a wasu rumfunan zaɓen jihar.

Tuni dai hukumar zaɓen ta ce ta ƙaddamar da bincike kan zargin rubuta sakamakon bogin a kan takardun rubuta sakamakon zaɓen.

Sannan ta buƙaci a kwantar da hankali da bin doka da oda da mutunta juna yayin da take dab da fara aikin karɓar sakamakon.

to sai dai tuni hukumae ta INEC ta fara barra sakamakon zaben ina a karamar hukumar Esan ta Yamma

APC – 12952

PDP – 11004

sai kuma karamar hukumar Owan ta Yamma

APC – 12277

PDP – 11284

Karamar hukumar Uhunmwode

APC – 8776

PDP – 9339

a karamar hukumar Ovia ta Arewa maso yamma kuwa

APC – 13225

PDP – 15311

sai kuma karamar hukumar Esan ta kudu maso Gabas

APC – 8398

PDP – 14199

haka kuma hukumar ta INEC ta bayyana sakamakon karamar hukumar Egor inda tace

APC – 16760

PDP – 14658

wadannan dai sakamakon manyan Jam’iyyun siyasa a jihar ne wadanda ke kan gaba wajen yawan kuri’a a zaben da ya guda a ranar asabar a jihar ta Edo.

PRnigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp