Home General Zabe Edo- IG ya bayar da umarnin takaita zirga-zirga a jihar

Zabe Edo- IG ya bayar da umarnin takaita zirga-zirga a jihar

Babban sifeton ‘yansandan Najeriya, Kayode Egbetokun ya bayar da umarnin taƙaita zirga-zirga a jihar Edo a lokacin zaɓen gwamnan jihar da za a gudanar ranar Asabar.

Cikin wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yansandan ƙasar, Olumiyiwa Adejobi ya fitar, babban sifeton ya bayar da umarnin taƙaita zirga-zirgar ababen hawa a kan tituna da ruwa da sauran hanyoyin sufuri tun daga ƙarfe 6:00 na safe zuwa 6:00 na maraice a ranar zaɓen.

To sai dai sanarwar ta iyakance masu muhimman ayyuka, ciki har da ‘yan jaridar da aka tantance da jami’an zaɓe da motocin ɗaukar marasa lafiya da masu kai ɗaukin gaggawa.

”Domin tabbatar da sahihancin zaɓen, babban sifeton ‘yansandan ya haramta wa duka jami’an tsaron da ke tsare ko raka manyan mutane zuwa rumfunan zaɓe ko cibiyoyin tattara sakamakon zaɓen”, kamar yadda sanarwar ta yi ƙarin haske.

Haka kuma sanarwar ta haramta aikin jami’an tsaron sa kai a faɗin jihar a lokacin zaɓen, haka kuma an haramta jiniya ga ababen hawan da ba a amince wa ba, domin tabbatar da kwanciyar hankalin masu zaɓe.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp