Home General Zabe Edo- IG ya bayar da umarnin takaita zirga-zirga a jihar

Zabe Edo- IG ya bayar da umarnin takaita zirga-zirga a jihar

Babban sifeton ‘yansandan Najeriya, Kayode Egbetokun ya bayar da umarnin taƙaita zirga-zirga a jihar Edo a lokacin zaɓen gwamnan jihar da za a gudanar ranar Asabar.

Cikin wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yansandan ƙasar, Olumiyiwa Adejobi ya fitar, babban sifeton ya bayar da umarnin taƙaita zirga-zirgar ababen hawa a kan tituna da ruwa da sauran hanyoyin sufuri tun daga ƙarfe 6:00 na safe zuwa 6:00 na maraice a ranar zaɓen.

To sai dai sanarwar ta iyakance masu muhimman ayyuka, ciki har da ‘yan jaridar da aka tantance da jami’an zaɓe da motocin ɗaukar marasa lafiya da masu kai ɗaukin gaggawa.

”Domin tabbatar da sahihancin zaɓen, babban sifeton ‘yansandan ya haramta wa duka jami’an tsaron da ke tsare ko raka manyan mutane zuwa rumfunan zaɓe ko cibiyoyin tattara sakamakon zaɓen”, kamar yadda sanarwar ta yi ƙarin haske.

Haka kuma sanarwar ta haramta aikin jami’an tsaron sa kai a faɗin jihar a lokacin zaɓen, haka kuma an haramta jiniya ga ababen hawan da ba a amince wa ba, domin tabbatar da kwanciyar hankalin masu zaɓe.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp