Home General Zabe Edo- IG ya bayar da umarnin takaita zirga-zirga a jihar

Zabe Edo- IG ya bayar da umarnin takaita zirga-zirga a jihar

Babban sifeton ‘yansandan Najeriya, Kayode Egbetokun ya bayar da umarnin taƙaita zirga-zirga a jihar Edo a lokacin zaɓen gwamnan jihar da za a gudanar ranar Asabar.

Cikin wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yansandan ƙasar, Olumiyiwa Adejobi ya fitar, babban sifeton ya bayar da umarnin taƙaita zirga-zirgar ababen hawa a kan tituna da ruwa da sauran hanyoyin sufuri tun daga ƙarfe 6:00 na safe zuwa 6:00 na maraice a ranar zaɓen.

To sai dai sanarwar ta iyakance masu muhimman ayyuka, ciki har da ‘yan jaridar da aka tantance da jami’an zaɓe da motocin ɗaukar marasa lafiya da masu kai ɗaukin gaggawa.

”Domin tabbatar da sahihancin zaɓen, babban sifeton ‘yansandan ya haramta wa duka jami’an tsaron da ke tsare ko raka manyan mutane zuwa rumfunan zaɓe ko cibiyoyin tattara sakamakon zaɓen”, kamar yadda sanarwar ta yi ƙarin haske.

Haka kuma sanarwar ta haramta aikin jami’an tsaron sa kai a faɗin jihar a lokacin zaɓen, haka kuma an haramta jiniya ga ababen hawan da ba a amince wa ba, domin tabbatar da kwanciyar hankalin masu zaɓe.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp