Home General Duk wanda ya ci zaɓen jihar Edo a ba shi – Tinubu

Duk wanda ya ci zaɓen jihar Edo a ba shi – Tinubu

Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya yi kira da dukkan masu ruwa da tsaki a jihar Edo da su tabbatar an martaba ƙuri’a da zaɓin mutanen Edo a zaɓen da za a yi gobe.

Tinubu ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a ta hannun mai magana da yawunsa, Bayo Onanuga.

“Shugaba Tinubu yana kira ga ƴan takara da jam’iyyu da magoya baya da su martaba tsarin dimokuraɗiyya da zaɓin mutane. Ya yi ammanar cewa mutanen za su yi zaɓi wanda suka ga ya dace da shugabantarsu,” kamar yadda sanarwar ta nuna.

Da yake kira ga Hukumar INEC da jami’an tsaro su kasance na kowa, Shugaba Tinubu ya ce dole kowane ɓangare ya gudanar da harkokinsa cikin lumana.

Tinubu ya nanata cewa domokuraɗiyya na cigaba ne idan akwai fahimtar juna da hakuri da kuma girmama tsarin ƙasa, inda ya ƙara da cewa INEC ta ɗauki alwashin gudanar da zaɓe sahihi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp