Home Labarai ‘Dole Najeriya ta ci gaba da gyaran tattalin arziki da take yi...

‘Dole Najeriya ta ci gaba da gyaran tattalin arziki da take yi tsawon shekara 15’

Bankin Duniya ya ce dole ne Najeriya ta ci gaba da yin tsare-tsaren da take kai a yanzu na tsawon aƙalla shekara 15, muddin tana son ɗorewar tattalin arzikinta.

Mataimaikin shugaban bankin, Mr Indermit Gill ne ya bayyana haka a wani taron tattalin arziki karo na 30 da aka yi a Abuja ranar Litinin.

Ya ce ya kamata gwamnati ta jajirce wajen ci gaba da tsare-tsarenta na yanzu domin shawo kan matsaloli da ƙasar ke fuskanta wanda kuma suka janyo rashin cigaba tsawon lokaci.

“Babu wani wayo da za a yi a batun gyaran tattalin arziki. Ya kamata Najeriya ta tsaya kan tsare-tsarenta na tsawon shekara 15. Tsare-tsaren da aka ɗauka yanzu ba za su yi daɗi ba ko kuma kawo sakamako mai kyau nan take, amma za su ɗora ƙasar kan turbar cigaba mai ɗorewa,” in ji shi.

Kalaman nasa na zuwa ne a daidai lokacin ƴan Najeriya ke ci gaba da nuna fushinsu kan cire tallafin man fetur da gwamnati ta yi da kuma tashin farashin dala.

Duk da cewa waɗannan tsare-tsare sun janyo tsadar rayuwa da kuma wahalhalu daban-daban ga ƴan ƙasar, jami’in na Bankin Duniya ya ce komawa baya ba zai haifar da ɗa mai ido ga tattalin arzikin ƙasar ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp