Home Labarai Najeriya ta yi asarar abincin da zai ciyar da mutum miliyan takwas...

Najeriya ta yi asarar abincin da zai ciyar da mutum miliyan takwas a 2024 – FAO

Hukumar abinci da bunƙasa aikin noma ta Majalisar Dinkin Duniya ta ce Najeriya ta tafka asarar tan 55,629 na abinci saboda ambaliyar ruwa a 2024.

Ƙididdigar da hukumar ta fitar ta nuna cewa asarar kayan abinci da aka tafka a Najeriya a bana ta isa a ciyar da mutum miyan takwas da rabi har tsawo wata shida.

Mataimakin shugaban hukumar a Najeriya, Salisu Mohammed, ya ce ɗumamar yanayi da hauhawar farashi da matsalar tsaro da kuma taɓarɓarewar tattalin arziki, na daga cikin abubuwan da suka addabi ɓangaren noma a Najeriya cikin shekarar nan.

Wannan ƙididdiga na zuwa ne albarkacin bikin Ranar Abinci ta Duniya, wanda ya mayar da hankali ga kira ga gwamnati ta haɗa hannu da ƙwararru wajen magance ƙalubalen ƙarancin abinci mai gina jiki a tsakanin al’umma.

Hukumar ta bayyana gamsuwa da matakan da gwamnati ke ɗauka wajen wadata ƙasa da abinci, amma ta yi gargaɗin cewa dole sai ta ƙara ƙaimi domin cim ma hakan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp