Home Labarai Kotun koli ta yi watsi da ƙarar da ke kalubalantar dokar kafa...

Kotun koli ta yi watsi da ƙarar da ke kalubalantar dokar kafa EFCC

Kotun kolin Najeriya ta ƙori ƙarar da wasu manyan alkalai na jihohi suka shigar, inda suke kalubalantar dokar da ta kafa hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa EFCC.

Tawagar alkalai mai mambobi bakwai da alkali Uwani Abba Aji ta jagoranta, sun amince da ƙorar ƙarar saboda ba ta cancanci a saurare ta ba.

Ƙarar wadda alkalai na jihohi 16 suka shigar, na neman a rushe EFCC.

Yayin da wasu jihohi suka janye daga ƙarar, wasu sun ki yin haka inda suka ce za su kalubalanci lamarin.

Jihohin da suka shigar da ƙarar sun haɗa da Ondo da Edo da Oyo da Ogun da Nasarawa da Kebbi da Sokoto da Jigawa da Enugu da Benue da Anambra da Filato da Cross River da kuma Niger.

Sai dai a lokacin sauraron ƙarar ranar 22 ga watan Oktoba, jihohin Imo da Bauchi da kuma Osun su ma sun shiga cikin ƙarar yayin da Anambra da Ebonyi da kuma Adamawa suka sanar da janye wa daga ƙarar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp