Wasu kalamai da suka fito daga bakin sakataren gwamnatin Najeriya, George Akume, na neman ‘yan siyasar arewacin ƙasar su jira har shekarar 2031 idan suna son yin takarar shugabancin ƙasar, sun janyo cece-kuce.
Mista Akume, ya faɗi hakan ne yayin hira da wani gidan talabijin a ƙasar, inda ya ce kamata ya yi a bar yankin kudancin Najeriya ya karasa shekaru takwas ɗin sa, kamar yadda itama Arewa ta yi lokacin mulkin shugaba Buhari.
Kalaman dai sun girgiza ƴan siyasar arewacin Najeriya, inda tuni aka fara mayar da martani.
Mai magana da yawun tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar, Abdulrashid Shehu Uba, ya ce kundin tsarin mulkin Najeriya ya bai wa kowaye damar fita don neman kujerar shugaban ƙasa.
“Babu wata yarjejeniya da aka yi ko kuma aka yadda za a tafi a kan wannan tsari. Idan su a APC sun yi wannan tsari mu ba haka yake a wajenmu ba. Ya kamata su tsaya su mayar da hankali kan zaɓen da suka ƙwace,” in ji Abdulrashid.
Kakakin na Atiku ya ce kowa na ganin yadda al’amura suka taɓarɓare a yanzu musammman ɓangaren tsaro da kuma tsadar rayuwa, inda ya ce da gwamantin APC ta yi aiki ba za ta fito ta ce kada wani ya yi takara ba.
Ya ce babu wani ɗan siyasa da suke tsoro kamar tsohon mataimakin shugaban ƙasar.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1462 days 4 hours 19 minutes 35 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1444 days 6 hours 1 minute 0 second
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com