Home General Majalisa ta sa a kamo Shugaban Kamfanin Julius Berger kan zargin N141bn

Majalisa ta sa a kamo Shugaban Kamfanin Julius Berger kan zargin N141bn

Majalisar Dattawa ta amince da ba da umarnin kamo mata Manajan Daraktan Kamfanin Gine-gine na Julius Berger, Mista Peer Lubasch.

Shugaban Majalisar, Sanata Godswill Akpabio ya ce ’yan majalisar sun ba da umarnin ne saboda sau uku Shugaban Kamfanin na kin amsa gayyatar majalisar.

Majalisar ta gayyaci shugaban kamfanin ne kan zargin ƙara Naira biliyan 141 a kuɗin aikin babban titin Itukpani zuwa Itu da ke jIhar Enugu, tare da yin watsi da aikin.

Da yake gabatar da ƙudurin, Mai Tsawatarwan Majalisa, Sanata Osita Ngwu, ya zargi kamfanin da ƙara kuɗin aikin daga Naira biliyan 54 zuwa biliyan 195.

Dan majalisar ta bayyana cewa daga bisani kamfanin ya kwashe kayansa daga wurin da ake aikin.

A kan haka ne sau uku majalisar ta na gayyatar shugaban kamfanin na Julius Berger ya zo ya yi bayani, amma ya yi watsi da su.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp