Majalisa ta sa a kamo Shugaban Kamfanin Julius Berger kan zargin N141bn

Majalisar Dattawa ta amince da ba da umarnin kamo mata Manajan Daraktan Kamfanin Gine-gine na Julius Berger, Mista Peer Lubasch.

Shugaban Majalisar, Sanata Godswill Akpabio ya ce ’yan majalisar sun ba da umarnin ne saboda sau uku Shugaban Kamfanin na kin amsa gayyatar majalisar.

Majalisar ta gayyaci shugaban kamfanin ne kan zargin ƙara Naira biliyan 141 a kuɗin aikin babban titin Itukpani zuwa Itu da ke jIhar Enugu, tare da yin watsi da aikin.

Da yake gabatar da ƙudurin, Mai Tsawatarwan Majalisa, Sanata Osita Ngwu, ya zargi kamfanin da ƙara kuɗin aikin daga Naira biliyan 54 zuwa biliyan 195.

Dan majalisar ta bayyana cewa daga bisani kamfanin ya kwashe kayansa daga wurin da ake aikin.

A kan haka ne sau uku majalisar ta na gayyatar shugaban kamfanin na Julius Berger ya zo ya yi bayani, amma ya yi watsi da su.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1463 days 38 minutes 10 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1445 days 2 hours 19 minutes 35 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com