Mene ya sa Gwamnonin Nijeriya ke butar ýan sandan Jiha

Majalisar tattalin arzikin Najeriya (NEC) ta karɓi rahotonnin matsayar gwamnonin jihohin ƙasar 36 kan kafa rundunonin ‘yansandan jihohi.

Majalisar tattalin arzikin ƙarƙashin jagorancin mataimakin shugaban ƙasa, ta yi zamanta a jiya Alhamis a fadar gwamnatin ƙasar da ke Abuja, inda gwamnoni da mataimakan wasu gwamnonin suka halarta tare da wasu masu bai wa shugaban ƙasa shawara.

Yayin da yake jawabi ga manema labarai a fadar gwamnatin jim kaɗan bayan kammala ganawar, gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya ce gwamnonin jihohin sun nuna cikakken goyon bayansu kan ƙirƙirar ‘yansandan jihohi saboda matsalolin tsaro da jihohin ke fama da su.

“Tabbas kowace jiha na da irin nata matsalolin da suka shafi tsaro, kuma da dama sun amince da kafa rundunonin ‘yansandan jihohi a matsayin mafita kan matsalolin,” in ji gwamnan na Kaduna.

To sai da majalisar ta dakatar da tattaunawa game da batun har sai a zamanta na gaba da za a yi cikin watan Janairun sabuwar shekara mai kamawa.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1463 days 12 hours 3 minutes 43 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1445 days 13 hours 45 minutes 8 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com