‘Ƴansanda sun kama mutum fiye da dubu 30 tare da ƙwato makamai a 2024

Babban sufeto janar na ƴansandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun ya ce jami’an rundunar sun kama waɗanda ake zargi da laifuka daban-daban har mutum 30,313, sannan sun ƙwato makamai 1,984 da alburusai 23,250 a shekarar 2024.

Shugaban ƴansandan ya bayyana haka ne a taron ganawa manema labarai a ranar Talata, 24 ga watan Disamba a Abuja.

A wata sanarwa da kakakin rundunar, ACP Olumuyiwa Adejobi ya fitar, ya ce sun bayyana nasarar da suka samu ne domin nuna irin shirin fuskantar baɗi da suke yi.

Shugaban ƴansandan ya yaba da ƙokarin jami’ansa da sadaukarwar da suka yi a shekarar, inda ya ƙara da cewa an samu nasarar ce tare da haɗin gwiwar sauran jami’an tsaro, inda ya ƙara da cewa ana buƙatar hakan domin tabbatar da tsaro mai inganci.

“Rundunar ƴansandan Najeriya ta samu nasarar daƙile masu aikata laifuka, inda ta samu nasarar kama waɗanda ake zargi da laifuka daban-daban guda 30,313 da ƙwato makamai 1,984 da alburusai 23,250, sannan mun ceci waɗanda aka yi garkuwa da su guda 1,581.”

Ya kuma yi kira ga hafsoshin rundunar su riƙa amfani da kimiyyar zamani domin aikinsu ya ƙara nagarta.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1464 days 13 hours 56 minutes 27 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1446 days 15 hours 37 minutes 52 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com