Gamayyar kungiyoyin arewacin Najeriya CNG, ta ce yankin arewa na da dimbin hanyoyin tara harajin da za su cike gurbin kudurin dokar sabunta haraji da ke gaban majalisar dattawa.
Wannan ya biyo bayan zama da kwararru kan hanyoyin raya tattalin arziki, da kungiyar ta yi a Abuja don neman mafita idan kudurin ya samu nasara.
CNG wacce ta sake nanata bukatar dakatar da kudurin don yi ma sa garambawul da zai dace da muradun kowane yanki, ta ce hakkin ya rataya a kan ‘yan Arewa a majalisa su tabbatar ba’a yi wa yankin sakiyar da ba ruwa ba.
Read Also:
Shugaban gamayyar kungiyoyin Jamilu Aliyu Charanci ya ce arewa ka iya samun dimbin kudin shiga daga albarkatun noma da kiwo matukar aka tabbatar ana karbar haraji kan duk buhun abinci da za’a fitar daga arewa a kuma daina kai shanu kai tsaye kudu maimakon haka a rika yankawa a na tura naman.
Wannan matsaya ta zo dai-dai da hangen tsohon sakataren gwamnati Mista Babachir David Lawan, wanda ya yi misali da arzikin noma da kiwo na jihar Adamawa “an tare ka an kirga shanu a ka ce kowace saniya ka biya haraji Naira dubu biyar, na yi lissafi a shekara ba za mu gaza samun akalla Naira Bilyan kusan dari ba. A na zuwa Mubi a na siyan shanu 300,000-400,000 to in ka kara N5000 a kai ya yi wani abu ne?”
A karshe Jamilu Charanci ya yi hannunka mai sanda ga ‘yan majalisar “al’umma su tashi su rike ‘yan majalisar su gam, wannan kudurin idan ya tsallake ba wadanda su ka cuce mu sai ‘yan majalisar mu, idan kuma a ka maido shi a ka janye shi to ku sani ba wanda ya taimake mu sai ‘yan majalisar mu”.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1462 days 18 hours 55 minutes 48 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1444 days 20 hours 37 minutes 13 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com