Home General Gwamnatin Nijeriya ta dakatar da Jirgi Max Air

Gwamnatin Nijeriya ta dakatar da Jirgi Max Air

Gwamnatin Najeriya ta hannun Hukumar kula da sufurin jragen sama ta ƙasar (NCAA) ta sanar da dakatar da ayyukan kamfanin jirgin sama na Max Air, bayan jirgin kamfanin ya yi hatsari a daren jiya Talata a jihar Kano.

Daraktan hulɗa da jama’a da kare haƙƙin abokan hulɗa na hukumar, Michael Achimugu – wanda ya fitar da sanarwar – ya ce dakatarwar za ta soma aiki ne a daren 31 ga watan Janairun 2025, domin bai wa hukumomin kamfanin damar tattance ayyukanta a cikin gida da ya haɗa da bincike kan kamfanin, ma’aikatansa, tsarin aikinsa da jiragensa, da kuma tattalin arziƙin kamfanin.

Achimugu ya kuma ce tuni hukumar tabbatar da kariya (NSIB) ta ƙaddamar da bincike kan musabbabin haɗarin na baya-bayan nan.

Jirgin Max Air samfurin B734 mai lambar rijista 5N-MBD, ya yi haɗari ne a yayin sauka a filin jirgin sama na Mallam Aminu Kano da ke Kano bayan tayarsa ta fashe a jiya Talata.

Duk da dai fasinjoji 53 da ke cikin jirgin sun fita lafiya, hukumar kula da filayen jiragen sama ta ƙasar (FAAN) ta rufe filin jirgin na wucin-gadi kafin buɗe shi a safiyar ranar Laraba.

Wannan ne karo na uku da ake samun haɗarin jirgin na Max Air a cikin wata uku.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp