Majalisar Dattawa ta gayyaci shugabannin tsaro kan zargin Amurka na ba wa Boko Haram kuɗi

Majalisar Dattawan Najeriya ta gayyaci shugabannin hukumomin bayanan sirri da na tsaron ƙasar da su gudanar da bincike kan zargin da ɗanmajalisar wakilan Amurka Perry Scott ya yi cewa hukumar raya ƙasashe masu tasowa ta Amurka, USAID, na samar da kuɗaɗe ga ƙungiyoyin ta’addanci ciki har da Boko Haram.

Majalisar ta zartar da hakan ne bayan da Sanata Mohammed Ali Ndume, ya gabatar da buƙatar binciken.

Ndume ya buƙaci majalisar ta ɗauki maganar da muhimmanci bisa la’akari da iallar da ‘yan ta’adda musamman ma Boko Haram suka yi.

Sanatan ya jaddada cewa cikakken bincike a kan lamarin zai iya kawo ƙarshen jita-jitar da ake yaɗawa a kan yadda ‘yan ta’adda suka iya kaiwa tsawon waɗannan shekaru suna ta’asa a ƙasar.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1462 days 9 hours 31 minutes 47 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1444 days 11 hours 13 minutes 12 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com