Home General ‘Yan bindiga sun yi wa wasu ƙauyuka biyar dirar mikiya a Kaduna

‘Yan bindiga sun yi wa wasu ƙauyuka biyar dirar mikiya a Kaduna

Rahotanni daga Najeriya na cewa ‘yan bindiga sun yiwa wasu kauyuka biyar da suka haɗa da Unguwan Tauka, Unguwan Lalle, Sannu da zuwa, Tsauni Dodo da Dandauka, dukkansu a karkashin karamar hukumar Kachia ta jihar Kaduna dirar mikiyan ranar Alhamis.

Wani shugaban al’ummar yankin wanda ya tabbatar wa Daily Trust ta wayar tarho faruwar lamarin, ya ce ‘yan bindigar sun kuma kai farmaki a wani yankin Fulani da ke ƙauyen Kubuwo, inda suka yi awon gaba da wasu matasa makiyaya guda uku.

Ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 6 na yamma, inda ‘yan bindigar ɗauke da makamai suka yi ta kai farmaki tare da tilasta wa mutanen kauyukan tserewa yayin da suka riƙa harbin kan mai uwa dawabi.

Ya ce ‘yan bindigar sun gudu ne daga farmakin da sojoji suka kai a dajin Kurutu-Azara, wanda ke kan iyaka da karamar hukumar Kagarko kuma suka yanke shawarar ƙaddamar da mummunan hari a kan al’ummar da abin ya shafa.

A cewarsa, ‘yan bindigar sun kona wata mota da babur guda a Unguwar Tauka a lokacin da sojojin suka dakile sace wasu mutanen kauyen a yankin.

Rundunar ‘yansandan yankin ta tabbatar da faruwar harin amma bata bayyana cewa ko harin ya yi sanadin rayuwa ko kuma jikkata ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp