Home General ‘Yan bindiga sun yi wa wasu ƙauyuka biyar dirar mikiya a Kaduna

‘Yan bindiga sun yi wa wasu ƙauyuka biyar dirar mikiya a Kaduna

Rahotanni daga Najeriya na cewa ‘yan bindiga sun yiwa wasu kauyuka biyar da suka haɗa da Unguwan Tauka, Unguwan Lalle, Sannu da zuwa, Tsauni Dodo da Dandauka, dukkansu a karkashin karamar hukumar Kachia ta jihar Kaduna dirar mikiyan ranar Alhamis.

Wani shugaban al’ummar yankin wanda ya tabbatar wa Daily Trust ta wayar tarho faruwar lamarin, ya ce ‘yan bindigar sun kuma kai farmaki a wani yankin Fulani da ke ƙauyen Kubuwo, inda suka yi awon gaba da wasu matasa makiyaya guda uku.

Ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 6 na yamma, inda ‘yan bindigar ɗauke da makamai suka yi ta kai farmaki tare da tilasta wa mutanen kauyukan tserewa yayin da suka riƙa harbin kan mai uwa dawabi.

Ya ce ‘yan bindigar sun gudu ne daga farmakin da sojoji suka kai a dajin Kurutu-Azara, wanda ke kan iyaka da karamar hukumar Kagarko kuma suka yanke shawarar ƙaddamar da mummunan hari a kan al’ummar da abin ya shafa.

A cewarsa, ‘yan bindigar sun kona wata mota da babur guda a Unguwar Tauka a lokacin da sojojin suka dakile sace wasu mutanen kauyen a yankin.

Rundunar ‘yansandan yankin ta tabbatar da faruwar harin amma bata bayyana cewa ko harin ya yi sanadin rayuwa ko kuma jikkata ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp