Harin ƴanbindiga ya hallaka mutane da dama a Taraba

Gwamnan jihar Taraba, Agbu Kefas, ya yi Alla-wadai da harin da ƴanbindiga suka kai kan al’ummomin Munga Lelau a karamar hukumar Karim Lamido na jihar, abin da ya janyo mutuwar mutane da ba a san adadinsu ba.

Ƴanbindigar sun kai harin ne a lokacin da mutane ke komawa gida daga gonakinsu.

Lamarin ya afku da yammacin ranar Juma’a, makonni kalilan bayan wasu da ake zargin ƴanbindiga sun kashe wasu manoma biyu a yankin Bandawa na jihar.

Gwamna Kefas ya ce ba za a lamunci kai irin waɗannan hare-hare ba, inda ya ce suna mayar da jihar baya maimakon ci gaba.

Ya gargaɗi masu kai harin da cewa za su ɗanɗani kuɗarsu.

Ya kuma ƙara nanata cewa yana duk mai yiwuwa domin tsare jihar daga hare-hare da ake kai wa.

Ya ƙara da cewa akwai buƙakatar haɗa-kai tsakanin al’umma da jami’an tsaro, musamman wajen bayar da bayanan da suka kamata.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1461 days 17 hours 15 minutes 44 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1443 days 18 hours 57 minutes 9 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com