Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo (DRC) da ƙasar Rwanda sun amince da yarjejeniyar zaman lafiya da nufin kawo ƙarshen rikicin da ke ci gaba da ɗaukar hankula a gabashin DRC, wanda ke da arzikin ma’adinai.
Ministocin harkokin wajen ƙasashen biyu ne za su rattaba hannu a yarjejeniyar wadda Amurka ta shiga tsakani don warware rikicin, a mako mai zuwa, ranar 27 ga Yuni.
Yarjejeniyar na da nufin a ƙwace makaman mayaƙa, da kuma dawo da damar agajin jin ƙai ga al’umma a yankin da rikicin ya addaba.
Yarjejeniyar ta ƙunshi sharuɗɗa masu muhimmanci kamar girmama cikakken ikon ƙasa da iyakokin juna da haramta ci gaba da faɗa da Janyewar mayaƙa daga yankunan da suka mamaye da ƙwace makamai da kuma taimakawa wajen dawo da ‘yan gudun hijira da waɗanda rikicin ya raba da muhallansu
Tun farkon shekarar nan ne mayaƙan M23 suka ƙwace manyan birane biyu mafi muhimmanci a gabashin DR Congo.
DR Congo ta zargi Rwanda da bayar da tallafi da makamai ga mayaƙan, amma Rwanda ta musanta hakan.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1463 days 13 minutes 5 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1445 days 1 hour 54 minutes 30 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com