Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya Tedros Adhanom Ghebreyesus, ya ce sama da mutane 40 ciki harda ƙananan yara da kuma ma’aikatan kiwon lafiya ne aka kashe a wani hari da aka kai a wani asibiti da ke Sudan a ƙarshen mako.
Ofishin hukumar ta WHO da ke Sudan, ya ce daga cikin waɗanda suka mutu akwai yara 6 da jami’an kiwon lafiya 5, sannan kuma anyiwa ginin asibitin mummunar ɓarna.
Read Also:
An dai kai harin ne kan Asibitin Al Mujlad da ke a yammacin Kordofan a ranar asabar da ta gabata, kusa da inda ake fafatawa tsakanin sojojin Sudan da dakarun RSF, a yaƙi da suke yi tun a watan Afrilun shekarar 2023.
Shugaban na WHO ya nemi a dakatar da kai wa ci biyoyin kiwon lafiya hari, duk da cewa bai ambaci sunan ɓangaren da ake zargi da kai wannan hari ba.
Sai dai ƙungiyoyin kare hakkin ɗan adam sun zargi wani jigin yaƙin sojojin Sudan marar matuƙi da kai wannan hari, da wata sanarwa da aka fitar a ƙarshen mako ta ce mutunen da suka mutu sun kai 9.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1470 days 22 hours 50 minutes 0 second,
Baptist School Students, Kaduna
1453 days 31 minutes 25 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com