Rundunar ƴansandan Abuja ta musanta garƙame hedikwatar PDP

Rundunar ƴansandan Abuja ta musanta rahotannin da ke cewa jami’anta sun karɓe iko da hedikwatar jam’iyyar PDP ta Wadata Plaza a ranar Litinin.

Rundunar ta ce tana son “ta nuna cewa babu gaskiya a rahotonnin sannan ba haka al’amarin yake ba. An kai jami’an ƴansandan ne zuwa wurin taron domin wanzar da doka da oda kamar yadda tsarin mulki ya tanada.

A wata sanarwa, rundunar ta ce “babu wani lokaci da jami’an ƴansanda suka kulle sakateriyar jam’iyyar ta PDP.”

A sanarwar, kwamishinan ƴan sanda na Abujar ya buƙaci kafafen watsa labarai da su yi kaffa-kaffa wajen tantance labarai kafin su wallafa shi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com