Akwai yiwuwar samun ruwan sama na tsahon kwanaki uku a Nigeria -NiMet

Hukumar hasashen yanayi ta Najeriya, NiMet ta yi hasashen samun mamakon ruwan sama da tsawa a wasu sassan ƙasar daga ranar Juma’a 18 ga watan Yuli zuwa Lahadi.

Cikin wani saƙon gargaɗi da hukumar ta wallafa a shafinta na X, ta ce za a fuskanci yanayi na saukar ruwan sama a wasu jihohin arewacin ƙasar da suka haɗa da Borno da Yobe da Kaduna da Bauchi da kuma jihar Gombe.

Haka kuma hukumar ta ce za a samu matsakaicin ruwan sama da tsawa a wasu sassan jihohin Adamawa da Yobe da Sokoto da Zamfara da Bauchi da Borno da Gombe da Jigawa da Kaduna da kuma jihar Taraba.

Hukuma ta NiMet ta kuma yi hasashen samun ruwan saman a wasu sassan jihohin Plateau da Nasarawa da Abuja da kuma Benue.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1492 days 5 hours 49 minutes 9 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1474 days 7 hours 30 minutes 34 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com