Home Labarai Sojojin Najeriya sun kashe ƴan Bindiga fiye da 100 a jihar Neja

Sojojin Najeriya sun kashe ƴan Bindiga fiye da 100 a jihar Neja

Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta tare da haɗin gwiwar ƴan sa-kai waɗanda ake kira bijilanti sun samu nasarar hallaka ‘yan bindiga biyo bayan wata fafatawa da suka yi  a tsakaninsu a ƙauyen Warari da ke Jihar Neja.

Rundunar ta ce artabun dai ya faru ne a ranar Talata wanda ta sami nasarar hallakafiye da ‘yan bindiga 100 waɗanda ke gilmawa a kan babura.

Lamarin ya faru ne bayan wani bayanin sirri da dakrun suka samu daga mazauna yankin game da hanyoyin da ‘yan bindiga ke bi don satar shanu.

Wannan ne ya bai wa sojojin damar kitsa kwanton-ɓauna da ya kai ga fafatawar da ta kai ga hallaka ƴan bindigan da dama.

wata shaidu sun tabbatarwa da PRNigeria cewa sojojin sun yi amfani da motoci masu sulke da makamai na zamani wanda ya ba su galaba a kan ‘yan bindigar.

Shugabannin al’umma a Warari sun tabbatar da girman rashin da ‘yan bindigar suka tafka, inda suka bayyana cewa gawarwakin wasu daga cikin su sun bazu a tituna da gonaki da dazuka da ke kewaye da yankin.

Neja na cikin jihohin Najeriya da ke fama da hare-haren ƴan bindiga masu kisa da kuma garkuwa da mutane domin neman kudin fansa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp