Home Labarai ACM ta yi Ala-wadai da satar dalibai a Neja

ACM ta yi Ala-wadai da satar dalibai a Neja

Kungiyar Arewa Connect Movement ta bayyana bakin ciki kan sabon harin da yan bindiga suka kai Makarantar Katolika ta St. Mary’s da ke kauyen Papiri a Karamar Hukumar Agwara ta Jihar Neja, inda suka yi awon gaba dalibai da ma’aikata da ba a san yawan su ba.

Kungiyar ta ce wannan lamari babban tashin hankali ne ga iyaye, yan uwa da kuma al’ummar kasa baki ɗaya.

A cikin sanarwar da shugaban kungiyar, Auwal Mahmud Durumin Iya, ya fitar, ya bayyana cewa a kwanan nan irin wannan abu ya faru inda aka sace dalibai mata 25 a Jihar Kebbi, kuma har yanzu ba a samu wani cigaba a kan lamarin ba, inda ya ce sake faruwar irin wannan al’amari a cikin lokaci kankani na sake nuna yadda matsalar tsaro ke kara ta’azzara.

Kungiyar ta bayyana cewa wannan kalubale ne babba ga gwamnati da hukumomin tsaro, tare da kira gare su da su sauya dabarun yaki da yan ta’adda domin kawo karshen wannan ta’asa wacce ta dade tana addabar al’umma.

A karshe, kungiyar ta mika sakon jaje ga Gwamnatin Tarayya, jihohin Neja da Kebbi, iyayen yara, da al’ummar ƙasa baki daya, tana mai rokon ALLAH Ya kawo dauki cikin gaggawa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp