Home Labarai Gwamnonin Arewacin Nijeriya sun yi Alhinin mutuwar sheik Dahiru Bauchi

Gwamnonin Arewacin Nijeriya sun yi Alhinin mutuwar sheik Dahiru Bauchi

Gwamnonin arewacin Najeriya sun nuna alhinin su bisa rasuwar jagoran ɗarikar Tijjaniyya a Najeriya Shiekh Dahiru Usman Bauchi wanda ya rasu a yau alhamis.

Gwamnan jihar Gombe Muhammad Inuwa Yahaya, wanda shi ne shugaban ƙungiyar ta gwamnonin jihohin arewa, ya bayyana Shehin a matsayin malamin da rayuwarsa da koyarwarsa suka taɓa rayukan miliyoyin mutane a tsawon shekaru.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnatin jihar Gombe Uba Misili ya fitar, Gwamnan ya ce Sheikh Dahiru Bauchi ya sadaukar da rayuwarsa ta tsawon shekara 100 wajen yaɗa ilimin addinin musulunci, inda ya taimaka wajen koyar da karatun al Qurani da Hadisi da fiqihu da sauran karatuka.

Shugaban ƙungiyar gwamnonin Arewacin Najeriyar ya kuma ce malamin ya taka muhimiyyar rawa wajen samar da zaman lafiya,da juriya, da haɗin kai da kuma tarbiyya a tsawon rayuwarsa.

Ya kuma miƙa ta’aziyyar ɗaukacin gwamnonin arewacin Najeriya ga iyalan marigayin, da mabiya ɗariƙar Tijjaniyyah, da ma alummar musulmi kan gagarumin rashin da aka yi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp