Sojoji Sun Ceto Basaraken Gargajiya na Plateau da Aka yi Garkuwa da shi

Sojoji Sun Ceto Basaraken Gargajiya na Plateau da Aka yi Garkuwa da shi

 

Wani basaraken gargajiya na kauyen Pinau da ke karamar hukumar Wase a jihar Filato, Dokta Dadda’u Ahmad, wanda aka yi garkuwa da shi da sanyin safiyar Talata tare da direbansa, sojojin da ke aiki da rundunar ‘Operation Safe Haven’ a kauyen sun ceto shi.

Kakakin rundunar ‘Operation Safe Haven’ da ke aikin tabbatar da zaman lafiya a Filato da Bauchi da wasu sassan Karina Manjo Ishaku Takwa ya tabbatar da faruwar lamarin.

Wani mazaunin kauyen Hassan Pinau ya ce, wasu ‘yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun yi garkuwa da basaraken gargajiya da aka ceto tare da direbansa a hanyarsu ta zuwa Wase.

Ya bayyana cewa jim kadan bayan samun labarin faruwar lamarin ga sojoji a kauyen, sai suka zage damtse tare da bin diddigin masu garkuwa da mutanen inda suka kwato bindigogi biyu, da babura uku.

Musa Hassan, wani ma’aikacin da ke kula da unguwanni a yankin, ya shaida wa jaridar The Nation cewa: “Ina tare da sojoji a lokacin aikin ceto. Sojoji da wasu ’yan unguwar ne suka dawo da basaraken gargajiyar kauyen da suka yi awon gaba da masu garkuwa da mutane zuwa daji.“Kowa yana farin ciki a ƙauyen yanzu. An yi musayar wuta tsakanin sojoji da maharan kafin a ceto wadanda abin ya shafa.

“Sojoji sun yi kokari. Muna rokon Allah Ya ba su ikon ci gaba da gudanar da ayyukan alheri da suke yi.”

Source: The Nation

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1183 days 10 hours 22 minutes 11 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1165 days 12 hours 3 minutes 36 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com