Home Labarai CISA ta yaba da matakin da Sojoji suka dauka kan barayin man...

CISA ta yaba da matakin da Sojoji suka dauka kan barayin man fetur A Nijeriya

Wata kungiyar mai zaman kanta mai lakabin Citizen’s Initiative for Security Awareness (CISA) ta yaba da tsauraran matakan da sojojin Nijeriya ke dauka na dakile barnar da masu fasa bututun mai, da kuma masu fashin teku da sauran masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa.

Haka kuma kungiyar ta kalubalanci kiran da wasu kungiyoyi suka yi na sallamar babban hafsan hafsoshin Nijeriya Janar Lucky irabo kan kone jirgin da aka kama da laifin satar mai a yankin Neja Delta.

PRNigeria ta ruwaito cewa, a makon da ya gabata ne, rundunar sojin kasar ta bayar da Umarnin lalata wani jirgin Ruwan dakon mai da aka kama da laifin satar mai a wasu boyayyun wurare a yankin Nijer Delta.

Kamen jirgin ya zo ne a daidai lokacin da ‘yan Nijeriya ke cigaba da fahimtar yadda ake gano bututun mai da aka samar ba bisa ka’ida ba, wanda ake satar danyen mai da su wanda akwo yanzu ba’a bayyana wadanda ke da alhakin samar da bututun ba.

ba tare da bata lokaci ba sojoji sun kona jirgin ruwa da aka kama da laifin cin amanar kasa domin aika sakon gargadi ga masu ta’adar cin dinduniyar tattalin arzikin Nijeriya.

A cewar CDS, an kama kayan aikin tare da lalata su a matsayin wata hanya ta nuna yunkurin da sojoji suka yin a magance munanan laifuka da satar mai.

Ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannu kodinetan kungiyar na kasa, Chidi Omeje da sakataren ta, Olasunkanmi Ogunbodede mai take “suka ga kokarin dakarun sojojin domin dakile kokarin da suke na yaki da masu yiwa tattalin Arzikin kasa ta’annati CISA tayi Allah wadai da kakkausar murya kan kokarin da wasu mutane ke yi ta hanyar amfani da rahoton kona jirgin ruwa da aka kama da laifin satar mai a matsayin wukar kugu don yin gangami.

Kungiyar ta bayyana cewa, wadannan mutane kuma suna kokarin yin katsalan kan ayyukan babban hafsan Tsaron kasar, Janar Lucky Irabor, wanda suke kira da a tsige shi  saboda yunkurin sa na daukar matakan da suka dace.

PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp