Home Labarai EU ta bayar da miliyan 75 don magance cutar mashaƙo a Najeriya

EU ta bayar da miliyan 75 don magance cutar mashaƙo a Najeriya

Ƙungiyar Tarayyar Turai ta bayar da tallafin dala 150,000, kwatankwacin naira miliyan 75 don yaƙi da yaɗuwar cutar mashaƙo a Najeriya.

Haka kuma gami taimaka wa al’umomin da suka kamu a jihohin Kano da Katsina da Legas da kuma Osun.

Tarayyar Turan ta ce ta ɗauki matakin ne sakamakon ƙaruwar yaɗuwar cutar a Najeriya tun farkon shekarar 2023.

Za a bayar da tallafin ne ga mutane sama da miliyan daya da rabi, inda za a fi bayar da fifiko kan mutanen da ke cikin haɗarin kamuwa da cutar.

Waɗanda ke zaune a wurare masu wahalar zuwa, kamar yadda ƙungiyar ta EU ta bayyana a wata sanarwa da ta fitar ranar Litinin.

Tallafin wani ɓangare ne taimakon da ƙungiyar ke haɗawa na tara asusu don magance aukuwar bala’o’i a ƙasashen duniya ta hanyar ƙungiyoyin Red Cross da Red Crescent.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp