Home General Kada ku shiga cikin ‘yan fashi da makami da sunan zanga -zanga...

Kada ku shiga cikin ‘yan fashi da makami da sunan zanga -zanga – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyeson Wike, ya bayyana cewa baza su bari a gudnar da zanga –zanga da ake shirin farawa daya ga watan agusta a birnin ba, saboda ranar 1 ga watan Agusta rana ce ta karrama sarakunan gargajiya a birnin.

Wike ya bayyana hakan ne yayin da yake ganawa da manema labarai bayan kamala taron tsaron birnin, wanda ya sami halartar karamar ministan birnin. Dr. Mariya Bunkure, jamián hukumar dake lura da birnin ta FCTA, shuwagabannin kananan hukumomi da sauran jamián tsaro a birnin.

Ministan ya bayyana cewa a wannan rana suna sa ran ziyartar aikin hanyar Saburi dake kusa da Dei-Dei a cikin kwaryar birnin na Abuja wato Abuja Municipal Area Council (AMAC), in da ya bukaci mazauna yankin kada su shiga cikin ýan fashi da makami don gudanar da zanga zanga.

“ka da ku bi wadannan ýan fashin da makami kan hanya, wadanda ke ikirarin gudanar da zanga –zanga. Babu wani abu zanga zanga. Abuja baza ta zama guda cikin yankunan da za’a gudanar da ita ba. Abinda kuke bukata shine shugabanci na gari, kuma muna yi muku abinda kuke bukata,’’

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp