Home General Kada ku shiga cikin ‘yan fashi da makami da sunan zanga -zanga...

Kada ku shiga cikin ‘yan fashi da makami da sunan zanga -zanga – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyeson Wike, ya bayyana cewa baza su bari a gudnar da zanga –zanga da ake shirin farawa daya ga watan agusta a birnin ba, saboda ranar 1 ga watan Agusta rana ce ta karrama sarakunan gargajiya a birnin.

Wike ya bayyana hakan ne yayin da yake ganawa da manema labarai bayan kamala taron tsaron birnin, wanda ya sami halartar karamar ministan birnin. Dr. Mariya Bunkure, jamián hukumar dake lura da birnin ta FCTA, shuwagabannin kananan hukumomi da sauran jamián tsaro a birnin.

Ministan ya bayyana cewa a wannan rana suna sa ran ziyartar aikin hanyar Saburi dake kusa da Dei-Dei a cikin kwaryar birnin na Abuja wato Abuja Municipal Area Council (AMAC), in da ya bukaci mazauna yankin kada su shiga cikin ýan fashi da makami don gudanar da zanga zanga.

“ka da ku bi wadannan ýan fashin da makami kan hanya, wadanda ke ikirarin gudanar da zanga –zanga. Babu wani abu zanga zanga. Abuja baza ta zama guda cikin yankunan da za’a gudanar da ita ba. Abinda kuke bukata shine shugabanci na gari, kuma muna yi muku abinda kuke bukata,’’

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp