Home General An saki yaran da gwamnati ta tuhuma da cin amanar ƙasa

An saki yaran da gwamnati ta tuhuma da cin amanar ƙasa

Wata kotu a Abuja ta soke tare da sakin yaran nan guda 26 tare sauran mutanen da gwamnatin ƙasar ta tuhuma da cin amanar ƙasa a ranar Juma’a.

Ana tuhumar mutanen ne 72 sakamakon zargin su da laifin ɗaga tutar Rasha a lokacin zanga-zangar matsin rayuwa ta #Endbadgovernace a Agusta. Waɗanda ake tuhumar dai sun musanta aika laifin.

Sakin ya biyo bayan umarnin da shugaba Tinubu ya bayar ranar Litinin cewa a sake su sannan kuma a miƙa su ga ma’aikatar jinƙan ƙasar domin kula da walwalarsu sannan ta sada su da mahaifansu tare da binciken dalilin da ya sa aka tsare su na tsawon lokaci alhali yara ne.

Tuni dai an miƙa yaran 26 tare da sauran manya fiye 50 ga ma’aikatar jinƙai.

Tunda farko dai ministan shari’ar Najeriya ya saka baki a batun inda ya nemi a mayar da kyas ɗin ofishinsa domin tabbatar da sakin yaran.

Wasu masu rajin kare haƙƙin ɗan adam sun shaida cewa yaran sun kasance a tsare a hannun ƴansanda tun watan Agusta, wani abu da ke janyo kiraye-kirayen a nema musu haƙƙinsu.

Ɗaya daga cikin iyayen yaran nan da gwamnatin Najeriya ta tuhuma da cin amanar ƙasa sakamakon zanga-zanga kan tsadar rayuwa ta ce ta yi farin ciki da umarnin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu da ya ce a sake su.

Kafin ta je Abuja, Fatima ta ce an kira ta an faɗa mata ɗaya daga cikin ‘ya’yan nata ba shi da lafiya. Bayan ta isa kuma, kullum sai ta je wurin da ake tsare da su.

“Tun da na zo Abuja ban koma gida ba, kullum sai na je wajensu. Wani lokacin ma sai na je na yi bara kafin na samu abin da zan kai musu.

“Lokacin da na fara zuwa, da kyar aka bari na ga ɗaya daga cikin yaran nan kuma sai da na ba da kuɗi. Wani lokacin N1,000 ma ba ta isa, korar mu suke yi har sai ka samu masu kirki ne za su ƙyale ka,” kamar yadda ta yi bayani.

Ta ce tun yaran suna ƙanana aurenta da mahaifinsu ya mutu, kuma yana can kwance yana jinya sakamakon cutar shanyewar ɓarin jiki.

Ƙungiyar kare haƙƙi ta Amnesty International ta ce kama yaran ya saɓa wa dokokin ‘yancin ɗan’adam na ƙasa da ƙasa, kuma yi kira ga Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya sake “nan take ba tare da wani sharaɗi ba”.

Malam Isa Sanusi, shugaban kungiyar a Najeriya, ya bayyana wa BBC cewar sun kuma nemi a biya diyya saboda “gallazawa da galabaitarwa da yaran suka fuskanta tsawon lokacin da ake tsare a cikin watan Agustan”.

Kwana ɗaya bayan sukar da gwamnatin ta sha, Antoni janar kuma babban lauyan gwamnatin Najeriya, Lateef Fagbemi, ya nemi rundunar ‘yansandan ta miƙa masa lamarin domin cigaba da bibiyar shari’ar.

A ƙarshen mako kuma sai ga Ministar Mata Imaan Sulaiman-Ibrahim ta ziyarci yaran, inda aka gan ta a hotuna tana raba musu ruwa da abinci tare da cin alwashin yi musu adalci.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp