Home Bincike Bincike: Shin da gaske ne wata matashiya na fuskantar hukuncin kisa a...

Bincike: Shin da gaske ne wata matashiya na fuskantar hukuncin kisa a Jihar Zamfara Saboda Ta Sauya Addini zuwa Kiristanci?

Ikirari: Wani rubutu da ya karade kafafen sada zumunta na zamani da kuma wasu rahotannin kafafen yada labarai sun yi ikirarin cewa wata mata mai kimanin shekaru 22 a duniya mai suna Zainab Muhamadu na fuskantar hukuncin kisa a jihar Zamfara, bisa zargin sauya addininta daga Musulunci zuwa Kiristanci.

Rahotanni sun ce wani mai hidimar ƙasa (NYSC) da aka ce ana kiransa Fasto Samuel, ya rinjayi Zainab ta sauya addininta bayan sun kulla dangantaka ta ruhi da juna.

Jaridar The Guardian ta wallafa labarin da taken: “Zamfara Woman Faces Death Penalty for Converting to Christianity.” Wato wata ‘yar Zamfara na fuskantar hukuncin kisa bisa Sauya Addini.

Lamarin ya jawo cece-kuce daga masana harkar shari’a da masu rajin kare hakkin ɗan adam, wadanda suka bayyana lamarin a matsayin take hakkin dan Adam, musamman na ‘yancin addini da kundin tsarin mulkin Najeriya ya tanada.

Tabbatar da Sahihancin Ikirari: Domin tantance sahihancin ikirarin, PRNigeria ta duba rahotanni daga kafafen yada labarai masu inganci. Sai dai, bayan The Guardian, wasu ‘yan kafafen labarai ne kadai suka wallafa irin wannan labari, kuma daga bisani wasu ciki har da Sahara Reporters sun goge labarin, lamarin da sanya shakku kan gaskiyar lamarin.

Bincike ya kara bayyana cewa Gwamnatin Jihar Zamfara ta fitar da sanarwar karyata wannan rahoto. Bisa ga rahoton jaridar Politics Digest, wanda bai ma wallafa labarin ba, gwamnatin ta bayyana ikirarin a matsayin “ƙarya kuma mai ɗauke da ruɗani,” tana zargin masu yada labarin da ƙoƙarin tayar da rikicin addini.

Shaidu: PRNigeria ba ta samu wata shaida ta gaskiya da ke nuna cewa an kama ko ana shari’a da wata mai suna Zainab Muhamadu a gaban kotun Shari’a a Zamfara ba.

Har ila yau, hoton da aka haɗa da labarin da ke yawo an gano cewa na wata mata ce mai suna Aalia Reeves, wata ‘yar asalin Amurka wadda ke ƙirƙirar abubuwan da suka shafi Musulunci a kafar TikTok.

Aalia ba ta taɓa zuwa Najeriya ba, balle a ce tana da alaƙa da jihar Zamfara ko wani lamari na sauya addini.

A cikin bidiyonta na TikTok, Aalia ta yi bayani yadda kishinta da sadaukarwarta ga addinin Musulunci ya taimaka wajen kyautata fahimtar mahaifiyarta Kirista game da addinin.

Kammalawa: Duk da yaduwar wannan labari da kuma wallafa shi da wasu kafafen yada labarai, babu wata shaida mai tushe ko tabbatacciya da ke nuna cewa akwai wata Zainab Muhamadu da ake tuhuma ko shari’a da ita a jihar Zamfara saboda sauya addini.

Hakanan hoton da ke cikin rahoton ba na Zainab ba ne, sai dai an dauki hoton Aalia Reeves domin ƙarfafa ƙaryar labarin.

Hukunci: labarin na Ƙarya ne, Babu wata shaida da ke nuna cewa gwamnatin Jihar Zamfara ta gurfanar da wata Zainab Muhamadu bisa sauya addini. Wannan ikirari ba shi da tushe, balle makama ya ta’allaka ne da ƙarya da satar hoto. Don haka, ƙaryane.

Daga PRNigeria

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp