Home Labarai Sanata Buba Ya Yi Kira da Zaman Lafiya Bayan Kama Masu Bata...

Sanata Buba Ya Yi Kira da Zaman Lafiya Bayan Kama Masu Bata Masa Suna

Sanata Shehu Buba ya yaba wa jami’an tsaro bisa kama mutanen da suka shirya wani kamfen na batanci damanufar bata masa suna da kuma wasu mutane.

Sanata Buba, wanda shi ne Shugaban Kwamitin Majalisar Dattawa kan Tsaro da Leken Asiri, ya shawarci ‘yan Najeriya da su kasance masu zaman lafiya, su dinga tabbatar da sahihancin bayani kafin yada shi, tare da mai da hankali kan matsalolin da ke damun al’umma.

“Na dade ina tsayawa kan zaman lafiya da jin daɗin al’ummarmu. Ina ƙaryata waɗannan zarge-zarge marasa tushe, kuma zan ci gaba da aiki don ci gaban Bauchi ta Kudu,” in ji shi.

Jami’an tsaro kwanan nan sun kama wasu masu tasiri a kafafen sada zumunta da ake zargin suna da hannu a kamfen ɗin bata suna da ake kai wa wasu ‘yan siyasa, ciki har da Sanata Buba.

An yi wannan kame ne bayan bincike mai zurfi da ya haɗa da bibiyar sakonnin kafafen sada zumunta da kuma asusun da ake dangantawa da yada bayanai na ƙarya da kalaman kiyayya.

Sanata Buba musamman an zarge shi da alaƙa da ‘yan bindiga. Duk da ya sha musantawa, waɗanda suka bata masa sunan suna ci gaba da yada ƙarya a kafafe daban-daban kafin hukumomi su shiga tsakani.

Masu laifin sun yi amfani da bidiyon da aka shirya da gangan don yada labaran ƙarya domin ɓata masa suna a cikin majalisa da kuma wajen shirye-shiryen zaben 2027.

Bayan an kama su a wasu jihohin Arewa, wasu daga cikin masu yada bayanan sun amsa cewa an yaudare su ta hannun mutanen da suka yarda da su. Waɗanda aka ba beli sun riga sun fito da bidiyo da rubuce-rubucen neman afuwa a shafukansu na kafafen sada zumunta.

A cikin wani bidiyo, ɗaya daga cikinsu mai suna Nasiru Ontop ya ce:

“Mun yi kuskure mai girma wajen yarda da Kibanna, wanda ba mu san shi sosai ba. Bayanansa duk na jabu ne. Sai bayan an kama mu muka fara shakkar gaskiyarsa.

An goge asusun TikTok ɗinsa yanzu. Mun aikata abin da bai dace ba bisa bayanan ƙarya da bayanansa na jabu, saboda haka muna neman afuwa ga Sanata Shehu Umar Buba da duk wanda abin ya shafa,” in ji shi.

Abdulrashid Abdullahi Kano, wanda ke anfani da shafin Facebook mai suna Vanguard Hausa, shima ya fitar da sanarwa yana cewa:

“Mun tabbatar cewa bidiyon da ke zargin Sanata Shehu Buba Umar ƙarya ne kuma na bata suna ne.

An ƙirƙire shi ne daga maƙiyan zaman lafiya domin su ɓata masa suna. Sanata Buba ya kasance mai himma wajen inganta zaman lafiya da sulhu, yana aiki tare da malamai da shugabannin al’umma wajen warware rikice-rikice a Bauchi ta Kudu.”

Zagazola Makama

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp