Home Taska An Ceto Marayu 15 Daga Hannun ƴan Bindiga a Jihar Kogi

An Ceto Marayu 15 Daga Hannun ƴan Bindiga a Jihar Kogi

Dahallukitab

An Ceto Marayu 15 Daga Hannun ƴan Bindiga a Jihar Kogi

 

Wasu ƴan bindiga sun sace yara 23 da mai ɗakin shugaban makaranta da gidan marayu na Dahallukitab da ke Zariagi, wani ƙauye da ke Kabba a kan titin Lokoja zuwa Okene da ke ƙaramar hukumar Adavi a jihar Kogi.

A cikin wata sanarwa da kwamishinan yaɗa labarai na jihar Kingsley Fanwo ya fitar a yau Litinin, ya ce an sace yaran ne a daren ranar jiya Lahadi.

Ya kuma ce jin kaɗan bayan samun rahoton harin, ƴan sanda tare da goyon bayan wasu jam’ain tsaro suka isa yankin, inda suka yi nasarar ceto yara 15.

Gwamnatin jihar na Allah-wadai da harin, inda ta bayar da tabbacin cewa jami’an tsaro na ci gaba da aiki wajen ceto sauran mutanen.

Sai dai sanarwar ta bayyana cewa makarantar wadda kuma take aiki a matsayin gidan marayu ba ta da rajista, inda ya ce irin waɗannan makarantu da ke irin waɗannan yankunan kuma gwamnati ba ta san da su ba, na kasancewa cikin barazana musamman a wannan lokaci na rashin tsaro.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp