Ƙasurgumin ɗan bindiga, Turji ya ɗauki Alhakin Kashe Sojoji a Jihar Sokoto
Ƙasurgumin ɗan bindigar nan, Bello Turji, ya bayyana a wani sabon bidiyo, inda ya ɗauki alhakin kisan wasu dakarun sojoji a Jihar Sakkwato.
Lamarin ya faru ne bayan da sojoji suka tashi zuwa garin Bargaja da ke Ƙaramar Hukumar Isa, sakamakon harin ’yan bindiga suka kai da sanyin safiyar ranar Asabar.
Mazauna yankin sun ce ’yan bindiga sun kai farmakin ne tsakanin ƙarfe 12:30 na dare zuwa 3 na safe, inda suka riƙa harbe-harbe, lamarin da ya jefa jama’a cikin tsoro.
Yayin da sojoji ke kan hanyar zuwa wajen domin kai ɗauki, wani bam da aka dasa a kan hanya ya tarwatsa motarsu a hanyar Isa zuwa Bargaja.
Rahotanni sun ce aƙalla sojoji biyu ne sun rasa rayukansu, yayin da wasu da dama suka jikkata.
A cikin bidiyon da ya fitar bayan aukuwar harin, Turji, ya ce yana murna da mutuwar abokan gabansa.
Read Also:
Ya kuma yi iƙirarin cewa mutanensa sun samu nasara a kan jami’an tsaro tare da ƙwato dabbobin da aka ƙwace a wajensu.
Rahotanni kuma sun nuna cewa an shiga damuwa a yankin kan cewa Turji na ƙara samun ƙarfi da kuma samun sabbin makamai a yankin iyakar Sakkwato da Zamfara.
Wani mai rajin kare haƙƙin jama’a, Basharu Altine Guyawa Isa, ya bayyana a shafinsa na Facebook cewa Turji da wasu kwamandojinsa suna tara mayaƙa tare da horar da su.
Ya kuma ce wasu mayaƙa masu alaƙa da Boko Haram sun shiga cikin ƙungiyar domin taimakawa wajen horo da kuma kai hari.
Ya ƙara da cewa ƙungiyar ta samu makamai masu hatsari ciki har da na’urar gani cikin dare.
Hukumomi ba su tabbatar da waɗannan zarge-zarge ba, kuma ’yan sandan Jihar Sakkwato ba su mayar da martani ba lokacin da aka nemi jin ta bakinsu.
Waɗannan rahotanni na ƙara haifar da fargaba a tsakanin mazauna wasu yankuna na Jihar Sakkwato da kewaye.











