Home Taska Ƙasurgumin ɗan bindiga, Turji ya ɗauki Alhakin Kashe Sojoji a Jihar Sokoto

Ƙasurgumin ɗan bindiga, Turji ya ɗauki Alhakin Kashe Sojoji a Jihar Sokoto

Ƙasurgumin ɗan bindiga, Turji ya ɗauki Alhakin Kashe Sojoji a Jihar Sokoto

Ƙasurgumin ɗan bindigar nan, Bello Turji, ya bayyana a wani sabon bidiyo, inda ya ɗauki alhakin kisan wasu dakarun sojoji a Jihar Sakkwato.

Lamarin ya faru ne bayan da sojoji suka tashi zuwa garin Bargaja da ke Ƙaramar Hukumar Isa, sakamakon harin ’yan bindiga suka kai da sanyin safiyar ranar Asabar.

Mazauna yankin sun ce ’yan bindiga sun kai farmakin ne tsakanin ƙarfe 12:30 na dare zuwa 3 na safe, inda suka riƙa harbe-harbe, lamarin da ya jefa jama’a cikin tsoro.

Yayin da sojoji ke kan hanyar zuwa wajen domin kai ɗauki, wani bam da aka dasa a kan hanya ya tarwatsa motarsu a hanyar Isa zuwa Bargaja.

Rahotanni sun ce aƙalla sojoji biyu ne sun rasa rayukansu, yayin da wasu da dama suka jikkata.

A cikin bidiyon da ya fitar bayan aukuwar harin, Turji, ya ce yana murna da mutuwar abokan gabansa.

Ya kuma yi iƙirarin cewa mutanensa sun samu nasara a kan jami’an tsaro tare da ƙwato dabbobin da aka ƙwace a wajensu.

Rahotanni kuma sun nuna cewa an shiga damuwa a yankin kan cewa Turji na ƙara samun ƙarfi da kuma samun sabbin makamai a yankin iyakar Sakkwato da Zamfara.

Wani mai rajin kare haƙƙin jama’a, Basharu Altine Guyawa Isa, ya bayyana a shafinsa na Facebook cewa Turji da wasu kwamandojinsa suna tara mayaƙa tare da horar da su.

Ya kuma ce wasu mayaƙa masu alaƙa da Boko Haram sun shiga cikin ƙungiyar domin taimakawa wajen horo da kuma kai hari.

Ya ƙara da cewa ƙungiyar ta samu makamai masu hatsari ciki har da na’urar gani cikin dare.

Hukumomi ba su tabbatar da waɗannan zarge-zarge ba, kuma ’yan sandan Jihar Sakkwato ba su mayar da martani ba lokacin da aka nemi jin ta bakinsu.

Waɗannan rahotanni na ƙara haifar da fargaba a tsakanin mazauna wasu yankuna na Jihar Sakkwato da kewaye.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dr Lawan Sani: Yadda Masanin Tsaron Intanet Ya Zama Sarkin Gumel: Daga Shuaib S. AgakaAllah ne Kawai Zai Iya Hana Tinubu Cin Nasara a 2027 — Datti"Dangantakar Farar Hula da Sojoji Itace Mabuɗi ga Tsaron Ƙasa da Shugabanci Nagari" — Tsohon CDS IraborRundunar Sojin Najeriya ta Binciki Zargin Cin Zarafin Jima'i da Aka yi wa Kyaftin a JosBabban Jami’in EFCC na Fuskantar Zarge-Zargen Cin Hanci da Dukiyar da ba a San Asalinta baƳan Sandan Legas Sun Kama Mutum 4 da Ake Zargi da Fashin Daji, Sun Kwato Wayoyin Hannu 25, Kwamfutoci da Kayan Ado na ZinareRundunar Sojin Ruwa Ta Rusa Wuraren Tace Mai Ba bisa Ka’ida Ba, Ta Kwato Lita 350 na AGO a Rivers2027: Yahaya Bello Ya Tara Masu Daidaita Ayyuka na A4A a Arewa ta Tsakiya Domin sake Zaban TinubuSojoji Sun Kama Mutum 2 da ake Zargi da Taimakawa Ƴan Ta’adda, Sun Kwace Kayayyakin Babur a YobePDP Ta Yi Gargadi Kan Zargin Tattara Katunan Zabe PVC da Bayanan Asusun Banki a GombeRundunar Sojojin Najeriya ta Sauya Manyan Janarori Zuwa Muhimman Mukamai na Aiki da DabaruHukumar INEC za ta ƙaddamar da Na’urar Bibiyar shirye-shiryen Zaɓen 2027 kai TsayeDaliban Tallafin Horarwa na Prnigeria Sun Ziyarci Emirate FM, Sun Samu Kyawawan Bayani Kan Watsa Labarai na DijitalNSCIA ta yi Allah Wadai da Nuna Bambancin Addini a Ci gaba da Tsare El-RufaiSarkin Ilorin Ya Yaba da Tallafin Horarwa na PRNigeria Wajen Shirya Masu Watsa Labarai na Nan Gaba
X whatsapp