Home Taska Matsalar Tsaro:  An Kashe Manoma 6 a Jihar Kaduna 

Matsalar Tsaro:  An Kashe Manoma 6 a Jihar Kaduna 

Matsalar Tsaro:  An Kashe Manoma 6 a Jihar Kaduna 

 

Harin ya sake jefa al’ummomin yankin cikin jimami da fargaba, duk da ƙoƙarin da ake yi na dawo da zaman lafiya.

Wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun kashe manoma shida yayin da suke aiki a gonakinsu a yankin Kujijiro da ke Gundumar Kuyello ta Ƙaramar Hukumar Birnin Gwari a Jihar Kaduna.

Ƙungiyar Birnin Gwari Emirate Progressives Union (BEPU) ta tabbatar da harin, tana mai bayyana lamarin a matsayin abin takaici da tayar da hankali.

A cikin wata sanarwa da shugaban ƙungiyar, Dakta Isa Muhammad, ya fitar, ya ce harin ya sake jefa al’ummomin yankin cikin jimami da fargaba, duk da ƙoƙarin da ake yi na dawo da zaman lafiya.

Ƙungiyar ta yi gargaɗin cewa ci gaba da kai hare-hare kan manoma na iya hana mutane komawa gonakinsu a wannan kakar noma, lamarin da ka iya shafar samar da abinci da kuma ƙara tsadar rayuwa.

BEPU ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta Jihar Kaduna da su ƙara kaimi wajen magance matsalar tsaro a Birnin Gwari da maƙwabtanta.

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, gwamnatin jihar da rundunar ’yan sanda ba su fitar da wata sanarwa kan lamarin ba.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban JosMatsalar Tsaro:  An Kashe Manoma 6 a Jihar Kaduna An Zargi Kwankwaso da Sayen Fom ɗin Takara na Kujeru 69 a Jam'iyyar PRPƘasurgumin ɗan bindiga, Turji ya ɗauki Alhakin Kashe Sojoji a Jihar SokotoMasu Iƙirarin Jihadi Sun Hallaka Manoma 11 a Jihar Borno 'Yan Bindiga sun ƙone shingen Jami'an NSCDC Tare da Garkuwa da Mutum 1 a Jihar KebbiTaron NUJ: Lokacin Da Manyan Jami’an Tsaro Suka Guji Yan Jarida Daga Yushau A. ShuaibSamar da Tsaro: Sojojin Najeriya sun Kama ƴan ƙasashen Wajen 46Ta'addanci: Za a Gurfanar da Mutane 400 a Gaban Kotun Tarayya da ke AbujaAn Ceto Matar Janar Rabe da ya Rasu a Hannun ƴan BindigaHauhawar Farashin Kayan Masarufi a Najeriya ya ƙaru Zuwa Kashi 15.93Rundunar Sojin Najeriya ta Gudanar da Hare-Hare Kan Maɓoyar ƴan Bindiga a Jihar Katsina
X whatsapp