An Ceto Matar Janar Rabe da ya Rasu a Hannun ƴan Bindiga
Iyalan marigayi Manjo Janar Rabe Abubakar mai ritaya wanda ya rasu a hannun ƴan bindiga a jihar Katsina sun tabbatar wa BBC cewa sun samu labarin sakin matarsa wadda aka kama su tare.
Read Also:
Kamar yadda BBC ta samu labari daga ɗaya daga cikin ƴaƴansa, yanzu haka suna kan hanyar zuwa gida inda ake dakon isowarsu.
Sun ce sojoji ne suka taho da mahaifiyar tasu, inda suka buƙaci su shirya mata kayanta kafin su ƙarasa.
Sai dai sun ce ba su da tabbacin inda za a kai ta daga nan.











