Home Taska Ta’addanci: Za a Gurfanar da Mutane 400 a Gaban Kotun Tarayya da...

Ta’addanci: Za a Gurfanar da Mutane 400 a Gaban Kotun Tarayya da ke Abuja

Court

Ta’addanci: Za a Gurfanar da Mutane 400 a Gaban Kotun Tarayya da ke Abuja

 

Aƙalla mutum 400 ne za a gurfanar a gaban Kotun Tarayya da ke Abuja a ranar Litinin din nan kan zargin aikata laifukan ta’addanci, a ɗaya daga cikin manyan shari’o’in ta’addanci da aka taɓa yi a Najeriya.

Shari’ar na nuni da wani muhimmin mataki a ƙoƙarin gwamnati na ƙarfafa ɗaukar alhaki da kuma magance matsalar tsaro da ƙasar ke fama da ita tsawon lokaci.

Waɗanda ake tuhuma na fuskantar zarge-zarge daban-daban da suka haɗa da kai hare-hare da tallafawa ayyukan ƙugiyoyin masu tsattsauran ra’ayi da ta’addaci.

Wannan na zuwa ne bayan wata babbar shari’a a watan Afrilun 2026, inda aka gurfanar da sama da mutane 500 kan zargin aikata laifukan ta’addanci kuma an samu kusan 400 da laifi.

Mahukunta sun ce wannan mataki na da nufin kammala sauran shari’o’i da kuma gurfanar da ƙarin waɗanda ake zargi domin a hukunta su.

Najeriya na ci gaba da fama da rikicin ta’addanci na tsawon shekaru 16, wanda ya yi sanadin mutuwar dubban mutane tare da raba sama da miliyan biyu da muhallansu, yayin da matsalar garkuwa da mutane ke ci gaba da ƙaruwa a sassa daban-daban na ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Samar da Tsaro: Sojojin Najeriya sun Kama ƴan ƙasashen Wajen 46Ta'addanci: Za a Gurfanar da Mutane 400 a Gaban Kotun Tarayya da ke AbujaAn Ceto Matar Janar Rabe da ya Rasu a Hannun ƴan BindigaHauhawar Farashin Kayan Masarufi a Najeriya ya ƙaru Zuwa Kashi 15.93Rundunar Sojin Najeriya ta Gudanar da Hare-Hare Kan Maɓoyar ƴan Bindiga a Jihar KatsinaZaben 2027: NDC ta Tsayar da Ɗan Kwankwaso Mataimakin ɗan Takarar Gwamnan KanoKotu ta Umarci INEC da ta Soke Rajistar ADC Tare da Jam’iyyu 4Manyan Tsofaffin Jami'an Soji 10 da Suka Rasa Rayukansu a Hannun ƴan Ta'addaTarihin Rayuwar Janar Rabe da ya Rasu a Hannun ƴan BindigaMatsalar Tsaro: Masu Zanga-Zanga Sun Tare Babbar Hanyar AbujaDuk Wanda aka Kama Yana Kasuwanci da 'Yan Ta'adda, za a ɗauke shi a Matsayin ɗan ta’adda - Christopher MusaFarashin ɗanyen Mai ya Faɗi Bayan Amurka ta Soke Sabbin Hare-Haren kaiwa IranAmurka ta yi sulhu kan yaƙin da ta ke yi da Iran - TrumpMajalisar Wakilan Najeriya ta Amince da ƙudirin Dokar Kafa ’Yan sandan JihaHukuncin da aka Yanke wa Masu Alaƙa da Sace ɗaliban Jihar Neja
X whatsapp