Home Taska Ta’addanci: Za a Gurfanar da Mutane 400 a Gaban Kotun Tarayya da...

Ta’addanci: Za a Gurfanar da Mutane 400 a Gaban Kotun Tarayya da ke Abuja

Court

Ta’addanci: Za a Gurfanar da Mutane 400 a Gaban Kotun Tarayya da ke Abuja

 

Aƙalla mutum 400 ne za a gurfanar a gaban Kotun Tarayya da ke Abuja a ranar Litinin din nan kan zargin aikata laifukan ta’addanci, a ɗaya daga cikin manyan shari’o’in ta’addanci da aka taɓa yi a Najeriya.

Shari’ar na nuni da wani muhimmin mataki a ƙoƙarin gwamnati na ƙarfafa ɗaukar alhaki da kuma magance matsalar tsaro da ƙasar ke fama da ita tsawon lokaci.

Waɗanda ake tuhuma na fuskantar zarge-zarge daban-daban da suka haɗa da kai hare-hare da tallafawa ayyukan ƙugiyoyin masu tsattsauran ra’ayi da ta’addaci.

Wannan na zuwa ne bayan wata babbar shari’a a watan Afrilun 2026, inda aka gurfanar da sama da mutane 500 kan zargin aikata laifukan ta’addanci kuma an samu kusan 400 da laifi.

Mahukunta sun ce wannan mataki na da nufin kammala sauran shari’o’i da kuma gurfanar da ƙarin waɗanda ake zargi domin a hukunta su.

Najeriya na ci gaba da fama da rikicin ta’addanci na tsawon shekaru 16, wanda ya yi sanadin mutuwar dubban mutane tare da raba sama da miliyan biyu da muhallansu, yayin da matsalar garkuwa da mutane ke ci gaba da ƙaruwa a sassa daban-daban na ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dr Lawan Sani: Yadda Masanin Tsaron Intanet Ya Zama Sarkin Gumel: Daga Shuaib S. AgakaAllah ne Kawai Zai Iya Hana Tinubu Cin Nasara a 2027 — Datti"Dangantakar Farar Hula da Sojoji Itace Mabuɗi ga Tsaron Ƙasa da Shugabanci Nagari" — Tsohon CDS IraborRundunar Sojin Najeriya ta Binciki Zargin Cin Zarafin Jima'i da Aka yi wa Kyaftin a JosBabban Jami’in EFCC na Fuskantar Zarge-Zargen Cin Hanci da Dukiyar da ba a San Asalinta baƳan Sandan Legas Sun Kama Mutum 4 da Ake Zargi da Fashin Daji, Sun Kwato Wayoyin Hannu 25, Kwamfutoci da Kayan Ado na ZinareRundunar Sojin Ruwa Ta Rusa Wuraren Tace Mai Ba bisa Ka’ida Ba, Ta Kwato Lita 350 na AGO a Rivers2027: Yahaya Bello Ya Tara Masu Daidaita Ayyuka na A4A a Arewa ta Tsakiya Domin sake Zaban TinubuSojoji Sun Kama Mutum 2 da ake Zargi da Taimakawa Ƴan Ta’adda, Sun Kwace Kayayyakin Babur a YobePDP Ta Yi Gargadi Kan Zargin Tattara Katunan Zabe PVC da Bayanan Asusun Banki a GombeRundunar Sojojin Najeriya ta Sauya Manyan Janarori Zuwa Muhimman Mukamai na Aiki da DabaruHukumar INEC za ta ƙaddamar da Na’urar Bibiyar shirye-shiryen Zaɓen 2027 kai TsayeDaliban Tallafin Horarwa na Prnigeria Sun Ziyarci Emirate FM, Sun Samu Kyawawan Bayani Kan Watsa Labarai na DijitalNSCIA ta yi Allah Wadai da Nuna Bambancin Addini a Ci gaba da Tsare El-RufaiSarkin Ilorin Ya Yaba da Tallafin Horarwa na PRNigeria Wajen Shirya Masu Watsa Labarai na Nan Gaba
X whatsapp